Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Tinubu ya naɗa Nuhu Ribaɗu a matsayin mai ba shi shawara kan tsaro

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Rahoto kai-tsaye

A'isha Babangida, Mukhtar Adamu Bawa and Abdullahi Bello Diginza

  1. Fiye da mutum 70 sun mutu a haɗarin jirgin ruwa a Girka

    Akalla mutane 79 ne suka mutu sannan aka ceto sama da 100 a yayin da wani jirgin ruwa na kamun kifi ya nutse a kudancin ƙasar Girka.

    Waɗanda suka tsira sun ce aƙalla mutum 750 ne suka makale a cikin kwale-kwalen, ciki har da ƙananan yara fiye da 100.

    Gwamnatin ƙasar ta ce lamarin na cikin mummunan abu mafi girma da ya sami `yanci rani, ta kuma ayyana zaman makoki na kwana uku.

    Hukumomin ƙasar sun ce ba su samu taimakon da suka buƙata daga ƙasashen duniya na ceto mutanen da lamarin ya shafa ba.

    Sun ce a maimakon hakan, sai aka riƙa zarginsu da rashin yin abin da ya dace don taimakawa.

    Wani jami'i a hukumar da ke kula da 'yanci rani a Girkan, ya shaida wa BBC cewa, an yi nasarar ceto mutum 104, sannan kuma bai tabbatar da rahoton ɓacewar wasu da dama ba.

    Jirgin kwale kwalen ya taso ne daga Libya inda ya kife tare da nitsewa a ɗaya daga cikin wuri mafi zurfi a tekun Bahar Rum.

  2. Yunwa na kashe mutane a Koriya ta Arewa

    Al'ummar Koriya ta Arewa sun shaida wa BBC cewa ana samun ƙarancin abinci a ƙasar.

    Lamarin da suke cewa na hadasa mutuwar wasu daga cikin al'ummomin ƙasar saboda yunwa.

    A wata tattaunawar sirri ta musamman da aka yi, an gano cewa ƙasar da ta fi zama saniyar ware a duniya na cikin mummunan yanayin da aka jima ba a fuskanci irinsa ba tun shekarun 1990.

    Wasu mutane uku a kasar sun ce mabarata na mutuwa a kan tituna, sannan babu abinci a wasu kasuwanni.

    Wata mata ta ce takan hakura da abinci don 'ya'yanta su ci.

    Haka shima wani mutum ya ce "a kauyenmu mutane biyar sun mutu, saboda tsananin yunwa."

    "A wani gida, matar ba ta da lafiya sosai, akwai yara biyu da suke rayuwa sakamakon baran da nake", in ji shi.

    Akwai damuwar da ake nunawa a kan cewa Koriya ta Arewan ta shafe watanni tana fama da karancin abincin.

  3. Assalamu alaikum

    Masu bin wannan shafin barkan mu da safiyar wannan rana ta Alhamis.

    Aisha Babangida ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokaci, domin kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a faɗin duniya, za mu fi mayar da hankali kan Najeriya da makwabtanta.

    Kuna iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.