Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Babu buƙatar shugabannin Najeriya su fita waje neman lafiya - Aisha Buhari

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi and Ahmad Tijjani Bawage

  1. An yi kuskure a lissafin kuɗin makaman da Amurka ta aika wa Ukraine

    Ma'aikatar tsaron Amurka ta ce ba ta kiyasta kudin alburusai da makamai masu linzami da ma sauran kayan yakin da aka aika Ukraine daidai ba tana mai cewa sun kai na biliyoyin daloli.

    Ta ce an samu kuskuren hakan ne saboda ma'aikatar ta kimanta tsoffin makaman da aka dauko a dakin ajiya a matsayin sabbi.

    Kuskuren da aka samu zai bai wa gwamnatin Amurka damar kara aikewa da wasu makaman ba tare da bukatar karin wasu kudade daga majalisar dokokin kasar ba.

    Amurka dai ta aike da makaman da kudinsu suka kai na fiye da dala biliyan 21 ga Ukraine tun shekarar 2021.

  2. Zimbabwe ta saki fursunoni sama da 4,000 don rage cunkoso a gidajen yari

    Gwamnatin Zimbabwe ta saki dubban fursunoni a ƙarƙashin shirin yin afuwa na shugaban ƙasar domin rage cunkoso a gidajen yarin ƙasar.

    Hukumar da ke kula da gidajen yarin Zimbabwe ZPCS ta ce fursunoni sama da 4,000 da aka sallama akasarin su maza ne.

    Sai dai an tsame wadanda suka aikata miyagun laifuka da kuma wadanda aka samu da laifin fashi da makami da cin amanar ƙasa da kuma laifukan da suka shafi zaman lafiya daga cikin waɗanda aka sakin.

    Gidajen yarin Zimbabwe na fama da matsanancin cunkoso.

    Matakin na zuwa ne gabanin babban zaɓen ƙasar da za ayi a watan Agusta.

    Shugaba Emmerson Mnangagwa na fafutikar ganin ya shawo kan matsalar tsadar rayuwa, hauhawar farashin kayayyaki da kuma ƙarancin wutar lantarki.

  3. Ƴan sanda a Ghana sun shigar da ƙara kan rashin ƙarin girma

    Wasu ƴan sanda 82 a Ghana sun shigar da ƙara a kotu suna tuhumar gwamnati da rashin yi masu ƙarin girma bayan sun gama karatu a ƙarkashin tsarin hutun karatu da albashi na kasar.

    A ƙarkashi shugabancin mataimakin sufeto, Kofi Osal ‘yan sandan na ikirarin cewa an hana su karin girma tare da daman shiga kwalejin ’yan sanda duk kuwa da cewa sun kammala karatu a zangon karatu na 2017/2018.

    Sun ce ba a yi musu adalci da matakin da aka dauka ba, sun kuma yi kira ga babban kotun Accra da ta tilasta wa hukumar ‘yan sanda ta tabbatar masu da ƙarin girmar

  4. Barka da warhaka

    Da fatan mun wayi gari lafiya.

    Wannan shafi zai riƙa kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Za ku iya zuwa shafukanmu na sada zumunta a facebook da instagram da twitter domin bayyana ra'ayoyinku kan labaran da muke kawo muku.