Hukumomi a jihar Borno da ke arewa maso gabashin
Najeriya sun ce ma’aikata sun koma bakin aikin gyaran manyan turakun wutar
lantarki, bayan da ‘yan Boko Haram reshen ISWAP suka tarwatsa manyan layukan
wutar ranar Asabar.
Hare-haren Boko Haram dai sun yi wa turakun wutar lantarkin
mummunar illa tsawon lokaci, abin da yasa birnin Maiduguri ke fama da rashin
wutar lantarki tsawon watanni, amma hukumomin jihar sun ce sun dukufa wajen
gyarasu. Ga karin bayanin da Zahraddeen Lawan ya aiko mana daga Abuja.
Hare-haren Boko Haram dai sun yi wa turakun wutar
lantarkin mummunar illa tsawon lokaci, abin da yasa birnin Maiduguri ke fama da
rashin wutar lantarki tsawon watanni, amma hukumomin jihar sun ce sun tukufa
wajen gyara su.
Wani mutum da ya bukaci a boye sunansa ya
shaida wa BBC cewa a ranar Asabar ne kungiyar Boko Haram reshen ISWAP suka
dasa wa manyan turakun hudu bam al’amarin da ya yi sanadiyar tarwatsewarsu, a
dai-dai kauyen Kuturu kusa da Auno cikin kaaramar hukumar Kondiga a jihar
Borno.
Sai dai mutum ya ce ya ga ma’aikata suna kokarin gyarasu.
Hon Babakura Abbajato, Kwamishinan yada labarai na
jihar Borno ta waya, ya tabbatar wa BBC cewa ana aikin gyaran manyan turakun
wutar.
Ya ce ba su da wutar lantarki a Maiduguri fiye da wata
shida, saboda haren-haren Boko Haram da suka yi sanadiyar tintsirewar turakun
wutar har guda takwas a baya, inda ya ce suna kan aikin gyaransu ne, sai ga shi
‘yan ISWAP sun sake lalata wasu.
Haka kuma Hon Babakura ya ce kamfanin mai na NNPC zai
samar da wata tashar wutar lantarki mai karfin mega watt 50 a cikin Maiduguri,
nan da wani lokaci karin akan kokarin da suke yi na dawo da hasken wutar
lanatarki a birnin Maiduguri da sauran sassan jihar.