Bidiyon Ku San Malamanku tare da Sheikh Muhammad Sulaiman Sulaiman

Bayanan bidiyo, Ku San Malamanku tare da Sheikh Muhammad Sulaiman Sulaiman
An wallafa

Sheikh Muhammad Sulaiman Sulaiman asalin ɗan Gombe ne amma akasarin rayuwarsa ya yi ta ne a garin Jos na Jihar Filato. Haka kuma akasarin karatun da malamin ya yi, ya yi sa ne a garin na Jos.

Malamin ya soma karatunsa na firamare a wata makaranta da ke wani ƙauye mai suna Umoko a Jihar Ribas da ke kudancin Najeriya. Bayan malamin ya kammala firamarensa sai ya kuma yi sakandare inda ya yi H.I.S wato Higher Islamic Studies a wancan lokaci inda ya yi karatun a garin Jos.

A lokacin da yake karatun na H.I.S, Sheikh Sulaiman ya haɗa abu biyu a lokaci guda inda ya rinƙa karatu a Arabic Teachers College Grade 3.

Bayan ya kammala, sai da taimakon Sheikh Musa Ibrahim Sagagi Malam Muhammad ya samu gurbin karatu a kwalejin ilimi ta Kano.

Malam ya shafe shekara uku yana karatu a kwalejin ilimi ta Kano inda ya samu takardar shaidar karatu ta NCE, inda a cewarsa, daga kansu aka soke yi wa ƙasa hidima ga waɗanda suka kammala NCE wanda hakan bai bar su sun yi NYSC ɗin ba.