Tsohon Shugaban Chadi Hissene Habre ya rasu

Asalin hoton, AFP
Tsohon Shugaban Chadi Hissene Habre ya rasu ranar Talata yana da shekara 79, a cewar Ministan Shari'a na Senegal, Malick Sall.
Mista Habre ya rasu ne a asibiti yayin da yake zaman gidan yari a Senegal bisa aikata laifukan yaƙi a ƙasarsa da kuma lalata rayuwar 'yan Adam.
Wata kafar yaɗa labarai ta Senegal ta ce ya rasu ne sakamakon cutar korona, kamar yadda kamfanin labarai na AFP ya ruwaito.
A lokacin da ya mulki Chadi tsawon shekara takwas, shugaban ya dinga murƙushe 'yan adawa, abin da ya jawo mutuwar mutum fiye da 40,000, a cewar masu bincike.
A shekarar 2016 ne wata kotu ta musamman - wadda ƙungiyar haɗin kan Afirka (AU) da Senegal suka kafa - ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai.
An zargi Habre da aikata fyaɗe da bautarwa da kuma bayar da umarnin kisa a lokacin da yake kan mulki daga 1982 zuwa1990. Sai dai ya musanta zarge-zarge.
Wata hukumar bincike da aka kafa a Chadi bayan an kifar da gwamnatinsa a 1990 ta ce gwamnatin tasa ta aikata kisan da ke da alaƙa da siyasa 40,000 da kuma azabtar da mutum 200,000 cikin shekara takwas.

Asalin hoton, AFP
Lokacin shari'arsa, waɗanda suka tsira sun bayar da labarin irin yadda jami'an sirri na gwamnatin Habre suka azabtar da su.
An mayar da ɗaya daga cikin cibiyoyin azabtar da mutane a matsayin wurin ninkaya.
Shedu sun ce an azabtar da mutane ta hanyar amfani da lanarki da ƙunar taba sigari da kuma amfani da gas a idanunsu.
A 1990 ƴan tawaye suka hamɓarar da shi, inda ya nemi mafaka a Senegal.
Bayan shekara 20, kotun Chadi ta zartar masa da hukuncin kisa a bayan idonsa kan laifukan yaƙi.
Lokacin da yake tsokaci game da mutuwarsa, Reed Brody, wanda ya jagoranci gangamin tabbatar da an gurfanar da sohon shugaban, ya ce "Tarihi ba zai taɓa mantawa da ɗaya daga cikin masu mulkin kama karya a duniya da suka kashe mutanensu."
Habre ya ƙwace mulki ne a 1982 bayan haɓarar da Goukouni Oueddei, tsohon ɗan tawaye wanda ya lashe zaɓe.
An ta yin hasashen cewa ya samu goyon bayan CIA, a matsayin babban mai adawa da gwamnatin tsohon shugaban Libya Muammar Gaddafi.
Juyin mulkinsa na ya zo ne a lokacin da ake cikin yaƙi da Libya kan takaddamar fili.
Hibre wanda ya samu goyon bayan Amurka da Faransa, sojojinsa sun kori dakarun Libya a 1983.












