Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu: Kotun hukunta mazajen da suka bar matansu tsawon lokaci a Nijar
An wallafa
Latsa hoton sama ku saurari cikakken shirin
A cikin shirinmu na musamman kan ci-ranin mutanen Tahoua na jamhuriyyar Nijar, AbdusSalam Ibrahim Ahmed ya ziyarci kotun da ke yin sasanci da hukunta mazajen da suka yi lalata da matan aure.
Yawan tafiye-tafiyen don neman kuɗi kan sa maza su bar matansu tsawon lokaci, abin da ke jawo wasu su yi amfani da wannan damar domin aikata kwartanci.
Shirin na zuwa muku ne a madadin filin Taɓa Kiɗi Taɓa Karatu.