Gane mini Hanya: Matsalar ilimin ƴaƴa mata a jihar Kebbi

An wallafa

Latsa hoton sama domin sauraren rahoton Haruna Ibrahim Kakangi.

Ilimin ƴa mace wani abu ne da ke da matukar amfani a cikin al’umma, sai dai tsawon lokaci ƙarancin sanya yara makaranta ya kasance ɗaya daga cikin manyan matsaloli a Najeriya.

Wannan matsala ta fi Kamari ne a Arewacin kasar inda miliyoyin yara mata kan gaza samun ilimi sanadiyyar talauci ko kuma dalilai na ala’ada. 

BBC ta ziyarci jihar Kebbi domin ganin yadda matsalar take.