Mota ta yi kwanciyar magirbi da 'yan PDP a Abuja

An wallafa

Rahotanni na cewa akalla mutane hudu ne suka jikkata yayin zanga-zangar da babbar jam'iyyar adawa a Najeriya, PDP ta gudanar a babban birnin Abuja.

An gudanar da zanga-zangar a harabar kotun kolin kasar wadda a makon jiya kotun ta kwace mulki daga hannun PDP ta bai wa APC a jihar Imo da ke kudu maso gabashin kasar..

An tayin kide-kide da raye-raye yayin zanga-zangar, haka zalika an yi ta wasa da motoci abin da ya janyo taho mu gama tsakanin motocin PDP biyu.

Lamarin ya faru ne a dai-dai sha-tale-talen da ke kan titin Shehu Shagari a birnin Abuja.

Bayanai na cewa an bar mutanen da abin ya rutsa da su a gefen titi da zimmar motar asibiti za ta kwashe su.

Ba dai a samu wani rikici ba tsakanin mabiya jam'iyya da jami'an tsaro ko kuma da mambobin wata jam'iyyar.