'Shekara 50 ina rayuwa da albarushin yakin Biyafara a wuyana'
An wallafa
Latsa hoton da ke sama domin kallon bidiyon:
Wani tsohon Saja mai ritaya a rundunar sojin Najeriya ya bayyana yadda aka harbe shi a wuya a lokacin yakin Biafra da aka yi shekara 50 da ta wuce.
Malam Abdullahi Umar ya bayyana cewa alburushin yana wuyansa kuma idan aka cire zai iya jawo masa mutuwar barin jikin, domin barushin ya hade da wata jijiyarsa.
Ya ce a da idan ya yi kaki yana fitar da jini amma yanzu ya bari.
Bidiyo: Mansur Abubakar