Ana jimamin cika shekara 20 da rasuwar Dokta Mamman Shata

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 2

Jama'a da dama musamman a kafofin sada zumunta na ci gaba da nuna alhini bayan cika shekara 20 da rasuwar shahararren mawakin Hausa Dokta Mamman Shata Katsina.

Shata ya rasu ne a ranar 18 ga watan Junin shekarar 1999 a asibitin koyarwa na Malam Aminu Kano da ke Kano.

Jama'a da dama a shafukan sada zumuntar na tunawa da shi da wakokinsa da gudunmuwar da ya bayar wajen ci gaban harshen Hausa da nishadantar da jama'a.

Wane ne Mamman Shata Katsina?

  • An haife Shata a garin Musawa a jihar Katsina a shekarar 1923
  • Ya yi tallan goro da alewa lokacin da yake saurayi
  • Ya shafe fiye da shekara 50 yana salon wakar baka
  • An rubuta dimbin takardun da kasidu game da rayuwarsa
  • Jami'ar Ahmadu Bello ta Zariya ta ba shi digirin girmamawa
  • Gwamnatin Najeriya ta ba shi lambar girmamawa ta MON
  • Ya yi wakoki a fannoni daban-daban na rayuwa
  • Ya yi dimbin wakoki wadanda ya ce shi kansa bai san adadinsu ba
  • Ya ziyarci kasashe da dama ciki har da Amurka da Birtaniya da Saudiyya
  • Ya bar 'ya'ya 19 da kuma jikoki da dama
  • An binne shi ne a Daura.

Ku ma za ku iya bayyana yadda za ku iya tuna da wannan shahararren mawakin a shafinmu na Twitter.