Ali Ndume ya rungumi kaddara
An wallafa
Latsa hoton sama domin kallon bidiyon
Sanata Ali Ndume ya rungumi kaddara bayan da ya fadi zaben neman shugabancin majalisar dattawa Najeriya, wanda Sanata Ahmed Lawan ya lashe.
An kuma zabi Sanata Omo-Agege na jam'iyyar APC a matsayin mataimaki, inda ya doke Sanata Ike Ekweremadu na PDP.
Tuni Ali Ndume da Ekweremadu suka taya mutanen da suka kayar da su murna.
Zaben ya haifar da ce-ce-ku-ce musamman bayan da jam'iyyar APC ta nuna goyon bayanta ga takarar Ahmed Lawan.