Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Man City ta doke Man Utd
Manchester City ta yi nasara a kan abokiyar hamayyarta Manchester United a wasan da suka yi gumurzu ranar Lahadi inda suka tashi wasan 2-1.
David Silva ne ya fara zura kwallo a ragar Manchester United a minti na 43 da fara fafatawar, yayin da Marcus Rashford ya farke wa kungiyarsa a minta na 45.
Bayan da aka dawo hutun rabin lokaci ne Nicolas Otamendi ya kara zabga kwallo ta biyu a ragar Manchester United a minta na 54.
City ta ci gaba da zama ta daya a teburin firimiya da tazarar maki 11 tsakaninta da mai bi mata baya Machester United.
Sauran sakamakon wasannin da aka buga a gasar a ranar Lahadi su ne:
- Southamton 1-1 Arsenal
- Liverpool 1-1 Everton
Karanta wadansu karin labarai