Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
COP27: Wata mashiya a Kenya ta bukaci a mayar da hankali kan Afirka
COP27: Wata mashiya a Kenya ta bukaci a mayar da hankali kan Afirka
An wallafa
Matasa da ke fafutukar kare muhalli a Kenya irin su Elizabeth Wathuti suna fatan taron da ake yi kan sauyin yanayi na COP27 a kasar Masar zai "yi adalci" ga mutanen da suke fama da tasirin sauyin yanayi.
Nahiyar Afirka ta yi fama da matsalolin sauyin yanayi a kwanakin baya bayan nan - kamar tsananin zafi da fari.
Ta ce "Kowa yana kiran taron da suna COP na Afirka saboda yana faruwa a nahiyar, sai dai ya kamata a kira shi da wannan suna ne saboda bukatar nahiyar Afirka ita ce ta kamata a fi mayar da hankali a kanta wajen daukar mataki".