Wa zai fuskanci kalubale tsakanin Guardiola da Amorim a Etihad?

An wallafa
Lokacin karatu: Minti 1

Sabon kociyan Manchester United, Ruben Amorin zai kai wa Pep Guardiola ziyara a babban wasan hamayya na ƙungiyoyin Manchester.

Ranar Lahadi za a kece raini tsakanin Manchester City da Manchester United a Etihad a Premier League.

City mai rike da kofin bara ta yi nasara ɗaya daga wasa 10 baya da ta buga a dukkan fafatawa daga ciki aka doke ta bakwai.

Hakan ya sa City ta yi kasa zuwa mataki na biyar a teburi da tazarar maki tara tsakani da Liverpool mai jan ragama, mai kwantan wasa.

Shi kuwa Amorim ya yi nasara uku a karawa shida a dukkan fafatawa, sai dai an doke United karawa biyu a jere a hannun Arsenal da kuma Nottingham Forest a Premier.

Hakan ya sa United wadda ke fatan komawa kan ganiya karkashin sabon koci ta yi kasa zuwa mataki na 13 a kasan teburin babbar gasar tamaula ta Ingila.

A cikin watan Nuwamba, Amorim ya doke City 4-1 a Champions League a Portugal lokacin da yake jan ragamar Sporting.

Wasan da aka buga a bayan nan tsakanin City da United:

Community Shield Asabar 10 ga watan Agusta 2024

  • Man City 1 - 1 Man Utd

English FA Cup Asabar 25 ga watan Mayu 2024

  • Man City 1 - 2 Man Utd

Premier League Lahadi 3 ga watan Maris 2024

  • Man City 3 - 1 Man Utd

Premier League Lahadi 29 ga watan Oktoba 2023

  • Man Utd 0 - 3 Man City