Shugaban Afirka ta Kudu na fuskantar tsigewa

An wallafa

Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu na fuskantar tsigewa bisa abin da wani kwamiti bincike a kasar ya gano cewa "mai yiyuwa" ya sabawa dokar kundin tsarin mulki a kan yadda ya tafiyar da batun wata sata a gonarsa.

Al’amarin ya ja hankalin jama’a ne a watan Yuni lokacin da tsohon jami’in leken asiri na Afirka ta Kudu, Arthur Fraser, ya zargi shugaban kasar da boye kudaden da aka sace na dala miliyan 4 a gonarsa.

Kudin da aka boye a cikin katifa a gonarsa ya sa jam'iyyun hammaya sun rika zarginsa da halata kudin haram.

Sai dai Shugaban na Afirka ta Kudu ya musanta aikata wani abu da ya saba wa doka.

Rahoton na kwamitin  da ya kunshi alkalai ya sa Shugaba Cyril Rampphosa ciikin wani yanayi na  tsaka mai wuya wanda sa yaki da cin hancin da rashawa a abubuwan da zai fi ba fifiko a lokacin gudanar da yakin neman zaben shugaban kasa.

 

Sai dai  duk da cewa  bai zama dole a yi amfani da shawarwarin da kwamitin  ya bayar ba amma jam'iyyun hammaya za su iya amfani da rahoton wajen yin kira da a kara  gudanar da bincike mai zurfi a kan zarge-zargen.

Kuma idan an same shi da laifi toh watakila wannan zai sa a tsige shi daga mukaminsa na shugaban kasa.

 

Rahoton wanda ya kushi manyan kundi guda uku  ya  sa ana tambayoyi a kan dalilin da ya sa Mr Raamophosa ya ajiye makudan kudade a gonarsa.

Da kuma  dalilin da ya sa ya rika jinkirin  zuwa caji ofis din 'yan sanda domin ya shigar da kara  sannan kuma  ana zarginsa da yin rufa-rufa

 

Haka kuma kwamitin  ya  ce akwai alamar tambya  game da bayanin da shugaban ya yi a kan cewa miliyoyin sun fito ne daga baunar da ya sayar wadda yake kiwo.

Sai dai kwamitin ya yi amannar cewa akwai tambayoyi da dama  da ba a amsa  ba kuma ya bayyana zarge-zargen da ake ta yi wa shugaban a matsayin al'amari mai matukar muhimamci.

 

Sai dai a martamin da ta mayar jam'iyyar ANC mai mulki  ta kira wani taro da manyan jiga-jigan kungiyar a ranar alhamis.

Duk da cewa ba a bayyana abubuwan da taron zai tattauna ba amma ana kyautata zaton rahoton na cikin abubuwan da taron nasu zai mayar da hankali a kai.

 

A daya bangaren kuma ofishin shugaba kasa ya ce Mr Ramophosa na nazari a kan shawarwarin  da kwamitin ya bayar kuma nan bada jimawa ba zai mayar da martini.