Hikayata: Labarin Buɗaɗɗiyar Wasiƙa 16/02/2025

Bayanan sautiLatsa hoton da ke sama domin sauraron shirin
Hikayata: Labarin Buɗaɗɗiyar Wasiƙa 16/02/2025
An wallafa

A Labarinmu na Hikayata 2024, a wannan makon mun kawo muku labarin Buɗaɗɗiyar Wasiƙa na Zulaihat Haruna Rano, wadda ke zaune Unguwar Rimi a birnin Kaduna.

Marubuciyar ta gina labarinta a kan wata matashiya marainiya mai hazaƙar karatu, wadda wani malamin jami'a ya so ƙulla mata mata sharri bayan da ta ƙi yarda ya yi lalata da ita.

Daga baya dai ɗalibar ta samu nasarar kuɓuta, bayan da ta rubuta buɗaɗɗiyar wasiƙa domin bayyana wa hukumar makaranta da abokan karatunta ainihin abin da ya faru.

Badriyya Tijjani Ƙalarawi ce ta karanta labarin.