Ku San Malamanku tare da Sheikh Abbas Hussain

Bayanan bidiyo, Taba hoton don kallon bidiyon
Ku San Malamanku tare da Sheikh Abbas Hussain
An wallafa

Ku San Malamanku ya tattauna da Sheikh Abbas Hussein, wani malamin addinin musulunci a Najeriya.

An haifi malamin a karamar hukumar Dala da ke jihar Kano kuma ya yi karatun zaure da na Islamiyya.

A cewarsa, ya tashi cikin harkar karatun addini kasancewar kakansu ya assasa wata makarantar allow adda mahaifinsu ke rike da ita.

Ya ce a makarantar ne ya sauke karatun Al-Qur’ani kuma ya yi karatu a hannun malamai da dama ciki har da Sheikh Shariff Zakariyya.

.