Ku San Malamanku tare da Sheikh Abbas Hussain
Ku San Malamanku tare da Sheikh Abbas Hussain
An wallafa
Ku San Malamanku ya tattauna da Sheikh Abbas Hussein, wani malamin addinin musulunci a Najeriya.
An haifi malamin a karamar hukumar Dala da ke jihar Kano kuma ya yi karatun zaure da na Islamiyya.
A cewarsa, ya tashi cikin harkar karatun addini kasancewar kakansu ya assasa wata makarantar allow adda mahaifinsu ke rike da ita.
Ya ce a makarantar ne ya sauke karatun Al-Qur’ani kuma ya yi karatu a hannun malamai da dama ciki har da Sheikh Shariff Zakariyya.




