..Daga Bakin Mai Ita tare da Fatima ta kwana Casa'in

Bayanan bidiyo, Latsa alamar da ke sama domin kallo
..Daga Bakin Mai Ita tare da Fatima ta kwana Casa'in
An wallafa

A wannan makon mun kawo muku tattaunawa da tauraruwa Fatima Mohammed Mustafa wadda aka fi sani a fim mai dogon zango mai suna kwana Casa'in da gidan talabijin na Arewa24 ke nunawa.

Fatima wadda ƴar asalin jihar Kaduna ce, da ke zaune a birnin Kano, ta fara harkar fim ne bayan haɗuwarta da wani abokinta a shafin sada zumunta wanda ya nemi da ta aike masa da muryarta domin tantance ta.