Gane Mini Hanya tare da Abdussalami Abubakar
Gane Mini Hanya tare da Abdussalami Abubakar
An wallafa
Shirin namu na wannan mako ya tattauna da tsohon shugaban mulkin sojin Najeriya janar Abdussalami Abubakar mai ritaya.
Wanda shi ne jakadan ƙungiyar Ecowas na masamman kan rikicin da ƙungiyar ke yi da sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar.
Cikin makon da ya gabata ne ya jagoranci tawagar Ecowas zuwa Nijar, inda suka tatauna da jagororin juyin mulkin da kuma hamɓararen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum.