Shirye-shiryen zaɓen gwamnan jihar Kogi
Shirye-shiryen zaɓen gwamnan jihar Kogi
An wallafa
Hukumar Zaɓe Mai zaman kanta a Najeriya, INEC ta fara raba kayayyakin aikin zaɓe a jihar Kogi gabanin za ben gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar 11 ga watan Nuwamba.
Jihar Kogi - wadda ke tsakiyar Najeriya - na ɗaya daga cikin jihohi ukun da za a gudanar da zaɓen a cikin wannan makon.
Wakiliyar BBC da ke jihar ta ce tuni jami'an hukumar zaɓen suka fara rarraba kayyakin zuwa ƙananan hukumomi daban-daban da ke faɗin jihar.
Haka kuma ta ce an girke jami'an tsaro masu tarin yawa a sassan birnin Lokojo domin tabbatar da tsaro ga kayyakin zaɓen.



