Yadda mazauna Maiduguri suka rungumi kekuna bayan cire tallafin fetur

Bayanan bidiyo, Latsa hoton sama ku kalli bidiyo:
Yadda mazauna Maiduguri suka rungumi kekuna bayan cire tallafin fetur
An wallafa

Kafin watan Mayun 2023, hawa keke tamkar abin dariya ne a titunan birnin Maiduguri na jihar Borno da ke arewa maso gabas - musamman ga magidanta.

Amma tun bayan ranar 29 ga watan na Mayu; lokacin da Shugaba Bola Tinubu ya sanar da janye tallafin man fetur a Najeriya, kekuna sun cika titunan birnin, wato babu talaka babu mai kuɗi.