Sabbin matakan rage zuban jini da ke kashe masu haihuwa

Bayanan sauti
Sabbin matakan rage zuban jini da ke kashe masu haihuwa
An wallafa

Wani bincike da aka wallafa a mujallar kiwon lafiya ta 'The Lancet' ta nuna cewa an samu rage fiye da rabin mutuwar mata, a sanadiyyar zuban jini bayan haihuwa a jamhuriyyar Nijar.  

An cimma hakan ne bayan daukar wasu matakai uku da wasu masu bincike suka yi, da suka hada da amfani da wani magani mara tsada.  

Matsalar zuban jini bayan haihuwa, ita ce matsalar da ta fi kowacce janyo mace-macen mata a kasashe masu karancin kudin shiga.

Inda mafiya yawan mace-macen ke faruwa a kasashen da ke kudu da hamadar Saharar Afrika da kuma kudancin Asiya.

Ita ma Najeriya da ke yankin yammacin Afrika tana fuskantar matsalar mace-macen mata sakamakon zuban jini bayan haihuwa.

Jami'ai a jihar Kaduna da ke arewacin kasar sun ce jihar ita ke kan gaba wajen samun matsalar a Najeriya.

Sai dai sun ce hukumomi na yungurin ganin an magance matsalar.