Abu uku da zan yi kan matsalar tsaro a Katsina - Dikko Radda

Bayanan bidiyo, Danna hoton sama ku kalli bidiyon:
Abu uku da zan yi kan matsalar tsaro a Katsina - Dikko Radda
An wallafa

Ɗan takarar gwamnan Jihar Katsina a jam'iyyar APC mai mulkin jihar, Dikko Umar Radda, ya ce akwai abu uku da zai saka a gaba wajen shawo kan matsalar tsaro a jihar.

Ɗan takarar ya bayyana hakan cikin wata hira ta musamman da BBC Hausa da muke kawo muku da 'yan takarar muƙamai daban-daban yayin da ake tunkarar babban zaɓe na 2023 a Najeriya.

Katsina na cikin jihohin arewa maso yammacin ƙasar da suka fi fuskantar hare-haren 'yan fashin daji da ke kashe mutane tare da ƙona gidajensu da gonaki haka kawai.

A watan Mayu mai zuwa Gwamna Aminu Bello Masari na APC zai kammala wa'adi na biyu a matsayin gwamna, inda babbar jam'iyyar adawa ta PDP da sauransu za su nemi ƙwace mulkin jihar.