Ku San Malamanku tare da Sheikh Tijjani Goni Muhammad
Ku San Malamanku tare da Sheikh Tijjani Goni Muhammad
An wallafa
Sheikh Tijjani Umara Gwani Muhammad malami ne da aka haifa kuma ya rayu a birnin Maiduguri na jihar Borno a arewacin Najeriya.
An haife shi a shekarar 1956, kuma ya yi karatu a makarantar Islamiyya ta Sheikh Abul Fathi da ke Maiduguri, kafin mahaifinsa ya kai shi garin Kaulaha na ƙasar Senegal inda ya yi sakandare.
Ya yi karatun kwaleji da na jami'a a birnin Tripoli na Libya, inda ya samu shaidar digiri na farko da na biyu a can.
Malamin ya faɗa wa BBC cewa ya fi ƙwarewa a fannin tafsirin Ƙur'ani da kuma Hadisi.



