Ku San Malamanku tare da Sheikh Tijjani Goni Muhammad

Bayanan bidiyo, Latsa hoton sama ku kalli bidiyo:
Ku San Malamanku tare da Sheikh Tijjani Goni Muhammad
An wallafa

Sheikh Tijjani Umara Gwani Muhammad malami ne da aka haifa kuma ya rayu a birnin Maiduguri na jihar Borno a arewacin Najeriya.

An haife shi a shekarar 1956, kuma ya yi karatu a makarantar Islamiyya ta Sheikh Abul Fathi da ke Maiduguri, kafin mahaifinsa ya kai shi garin Kaulaha na ƙasar Senegal inda ya yi sakandare.

Ya yi karatun kwaleji da na jami'a a birnin Tripoli na Libya, inda ya samu shaidar digiri na farko da na biyu a can.

Malamin ya faɗa wa BBC cewa ya fi ƙwarewa a fannin tafsirin Ƙur'ani da kuma Hadisi.