Ku San Malamanku tare da Farfesa Yahuza Abdullahi Muhammad

Bayanan bidiyo, Latsa alamar da ke sama domin kallo
Ku San Malamanku tare da Farfesa Yahuza Abdullahi Muhammad
An wallafa

A wannan makon za mu kawo muku Sheikh Farfesa Yahuza Abdullahi Muhammad a filinmu na Ku San Malamanku wanda malami ne a birnin Maiduguri.

Farfesa Yahuza ya halarci makarantar harshen larabci da addinin Musulunci unguwar Agege da ke jihar Legas.

Malamin ya samu gurbin ƙaro karatu a ƙasar Syria inda daga baya ya koma ƙasar Libya domin samun shaidar karatun digiri.

Ya koyar a sashen koyar da Larabci a jami'ar da ke Maiduguri a jihar Borno inda kuma har yanzu a can yake koyarwa.

Shehun malamin ya yi karatu zaure da na zamani inda ya samu ilimi a wurin malamai da dama.

Farfesa ya ƙware a fannin harshen Larabci da fassara da kuma ilimin rabon gado.