Burina na ga Kanawa na taka leda a kulob ɗin duniya - Coach Hyda

Bayanan bidiyo, Na so zama ƴar ƙwallo amma raunin da na ji ya sa na zama kociya - Coach Hyda
Burina na ga Kanawa na taka leda a kulob ɗin duniya - Coach Hyda
An wallafa

Hyda Ahmad Ghaddar mai shekaru 27 da haihuwa kociya ce da horar da matasa ƙwallon ƙafa a ƙungiyarta mai suna 'Breakthrough Football Academy'.

Matashiyar ta fara buga ƙwallo ne tun tana ƴar shekara shida da haihuwa tare da ƴan uwanta a ƙofar gida.

An haifi Hyda a Lebanon amma iyayenta sun koma birnin Kano a lokacin da take ƴar watanni biyu, inda ta shafe shekara 16 a Kano kafin daga baya ta sake komawa Lebanon ɗin bayan kammala karatun jami'a.

"Babban burina shi ne samun wasu daga cikin waɗanda nake bai wa horo sun yi fice a duniyar ƙwallo." In ji Hyda Ahmad.