Burina na ga Kanawa na taka leda a kulob ɗin duniya - Coach Hyda
Burina na ga Kanawa na taka leda a kulob ɗin duniya - Coach Hyda
An wallafa
Hyda Ahmad Ghaddar mai shekaru 27 da haihuwa kociya ce da horar da matasa ƙwallon ƙafa a ƙungiyarta mai suna 'Breakthrough Football Academy'.
Matashiyar ta fara buga ƙwallo ne tun tana ƴar shekara shida da haihuwa tare da ƴan uwanta a ƙofar gida.
An haifi Hyda a Lebanon amma iyayenta sun koma birnin Kano a lokacin da take ƴar watanni biyu, inda ta shafe shekara 16 a Kano kafin daga baya ta sake komawa Lebanon ɗin bayan kammala karatun jami'a.
"Babban burina shi ne samun wasu daga cikin waɗanda nake bai wa horo sun yi fice a duniyar ƙwallo." In ji Hyda Ahmad.



