Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Dembele ya murmure zai fafata da Arsenal
Ɗanwasan gaba na Paris St-Germain Ousmane Dembele yana cikin tawagar da za su fafata da Arsenal a karawa ta biyu zagayen dab da ƙarshe a gasar Zakarun Turai.
PSG ta tabbatar da cewa ɗanwasan ya murmure kuma zai haska a wasan da za ta karɓi baƙuncin Arsenal a Paris.
Dembele ya ɗan samu rauni ne a cinyarsa a fafatawar farko da PSG ta doke Arsenal ci 1-0 a Emirates.
An sauya ɗanwasan bayan hutun rabin lokaci sakamakon raunin da ya ji.
Ɗanwasan mai shekara 27 wanda ya ci wa PSG ƙwallonta a raga, bai buga wa PSG wasan da ta sha kashi ba a Lig 1 hannun Strasbourg, amma ya fito atisaye a ranar Litinin.
"Ya yi atisaye tare da mu a kwanaki biyu," in ji kocin PSG Luis Enrique.
Ya ce ɗanwasan zai haska a wasan ranar Laraba da Arsenal.
Dembele wanda ya koma taka leda PSG daga Barcelona a 2023, shi ne ya fi yawan cin ƙwallaye a raga a PSG inda ya zuwa ƙwallo 33 a dukkanin wasannin da ya buga wa ƙungiyar a kakar bana.