Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.
Qatar 2022: An sauya lokacin buga wasa tsakanin Najeriya da Ghana
Hukumar kwallon kafa ta Afrika ta sanar da takwararta ta Najeriya cewa an sauya ranakun da tawagar Super Eagles za ta kara da Black Stars na Ghana, a wasan neman gurbin zuwa gasar cin kofin duniya cikin watan Nuwamba.
Daraktan sadarwa na NFF Ademola Olajire ne ya fitar da sanarwar, wadda ke cewa ''an sauya lokacin da za a buga wasannin share fagen zuwa gasar cin kofin duniya na Qatar 2022 tsakanin Najeriya da Ghana.''
A baya an shirya cewa Super Eagles da Black Stars za su buga gida da waje a ranakun 24 da 27 ga watan Maris.
To amma yanzu za a fara buga wasan farko ne a filin Cape Coast na Ghana a ranar 25 ga watan na Maris, kafin a tafi filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja a ranar 29 ga watan na Maris.
Bayan kammala wasannin biyu za a san wanda ya samu gurbin zuwa gasar cin kofin duniya da za a yi a Qatar cikin watan Nuwamba.
Kasashen biyu sun dade ana damawa da su a fagen kwallon kafa a nahiyar Afrika, to sai dai tafiyar su bata yi nisa ba a gasar cin kofin nahiyar ta AFCON da ba a jima da kammalawa ba a Kamaru.