An yi gasar Al Kur’ani ta ƴan ƙasa da shekara 13 a Ghana

An wallafa

Latsa hoton sama domin sauraren shirin

An gudanar da gasar karatun Al Kur`ani ta ƙasa a Ghana a karon farko a Accra, tsakanin `ƴan kasa da shekara 13 daga yankuna uku na ƙasar da suka ƙunshi yankin Ashanti da kuma arewacin Ghana.

Yara biyar ne daga kowanne yanki suka samu nasarar zuwa zagayen ƙarshe na wannan gasa, inda suka fafata tsakaninsu a ɗakin taro na ƙungiyar malamai ta kasa.

Wakilin BBC na Ghana Fahd Adam ya halarci gasar kuma ya aiko da rahoto na musamman.