Rikicin jam’iyyar APC da makomarta a zaɓen 2023

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don sauraron shirin:

Babban burin jam`iyyar siyasar da ta kafa gwamnati shi ne ta dade tana jan-zarenta.

Jam`iyyar APC mai mulki a Najeriya za ta kammala wa`adin mulkinta na biyu ne a shekara ta 2023, wannan ne ya sa ta dukufa wajen baza saiwarta a sassan kasar domin ta dore da mulki.

Sai dai kuma wasu na ganin cewa tana da babban kalubale a gabanta, sakamakon rashin cika wasu daga cikin muhimman alkawuran da ta yi wa `yan kasar, musamman ma maganar inganta tsaro, ga kuma ce-ce-ku-cen da ake yi a kan wadansu kararraki da kuma yankin da ya kamata ya karbi mulkin kasar.

Gwamnan jihar Ekiti, Kayode Fayemi shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya, kuma jigo a jam`iyyar APC.

A filin Gane Mani Hanya, Ibrahim Isa ya tattauna da shi a kan yadda yake kallon makomar jam`iyya mai mulkin a babban zaben da ke tafe: