Ra'ayi Riga: Ce-ce-ku-ce kan faduwar jarrabawar JAMB a Najeriya

An wallafa

Latsa alamar lasifikar da ke sama domin sauraron tattaunawar

A wannan makon shirin Ra'ayi Riga ya mayar da hankali ne kan yadda ƴan Najeriya da dama musamman ɗalibai suka yi ta kokawa kan rashin nasarar da suka yi a jarrabawar shiga manyan makarantu ta ƙasar wato JAMB, lamarin da ya jawo ce-ce-ku-ce a ƙasar.

Shirin ya tattauna da masu ruwa da tsaki a harkar ilimi don gano wadanne dalilai suka janyo haka kuma me hakan yake nufi ga makomar karatu a jami'oi da sauran manyan makarantu.