Yadda gubar dalma ta kashe yara 1,000 cikin shekara 12 a Zamfara

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Bayan shafe shekara 12 a jihar Zamfara da kungiyar likitoci ta Doctors Without Borders ta yi, a wannan makon MSF din ta bar jihar.

Ta fice ne bayan samun nasarar shawo kan annobarf mace-macen da gubar dalmar ta jawo.

MSF ta ce cikin wadannan shekaru yara 1,000 ne suka rasa rayukansu.