Zamfara: Ta'asar da ƴan bindiga suka yi a Kuryar Madaro

An wallafa

Latsa hoton sama domin kallon bidiyon

Ƴan bindiga sun abka garin Kuryar Madaro da ke cikin ƙaramar hukumar Kauran Namoda a jihar Zamfara inda suka kashe mutane da dama tare da ƙone motoci da gidaje.

Wasu mazauna yankin sun shaida wa BBC Hausa cewa maharan sun shiga garin ne da misalin ƙarfe 10:00 na dare inda suka shafe sa'o'i suna ta'asa a garin.

Wani mazaunin garin ya ce sun ƙirga gawar mutum 19 zuwa yanzu waɗanda ƴan bindigar suka kashe.

Sannan sun kwashi abinci a shagunan mutane da dabbobi.

Ƴan sandan Zamfara sun tabbatar da harin, inda suka ce sun tura jami'ansu.