Bidiyo: Ina mafita kan sace-sacen ɗalibai a makarantun Najeriya?

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

A wannan bidiyo, Abdulbaƙi Jari ya yi duba kan batun satar ɗalibai da yake neman zama ruwan dare gama duniya a arewacin Najeriya.

Daga watan Disamban 2020 zuwa yanzu an ƙiyasta cewa ƴan bindiga sun sace ɗalibai sama da 1,000 a jihohin Katsina da Kebbi da Neja da Kaduna da kuma Zamfara.

Sai dai tuni an ceto wasu yayin da har yanzu wasu ke hannun ƴan bindigar.