Bidiyon martanin Sheikh Abduljabbar Kabara kan hana shi wa'azi

An wallafa

Ku latsa hoton da ke sama don kallon bidiyon:

Sheikh AbdulJabbar Sheikh Nasir Kabara ya bayyana dakatarwar da gwamanatin Jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya ta yi masa daga yin wa'azi da rufe masallacinsa da cewa "zalunci ne".

Shiekh Abduljabbar ya faɗa wa BBC cewa duk da ita gwamnati da kanta, ta bakin kwamishinan Ilimi na jihar, ta tabbatar da abin da ake yi masa zalunci ne, amma ta dakatar da shi ba tare da ba shi damar kare kansa ba.

Abduljabbar dai na waannan kalami ne biyo bayan rufe makarantarsa da masallacinsa da gwamantin Kano ta sanar da yi a ranar Laraba tare da haramta saka karatunsa a kafafen sada zumunta da na yaɗa labarai a jihar.