Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Majalisar Dattijan Najeriya ta tantance ƙarin ministocin Tinubu

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Ahmad Tijjani Bawage and A'isha Babangida

  1. Ma'aikatan asibiti sun tsunduma yajin aiki a Amurka

    Sama da ma'aikata dubu saba'in da biyar ne da ke aiki a daya daga cikin manyan ma'aikatan kiwon lafiya na Amurka sun fara yajin aikin kwanaki uku.

    Yajin aikin ya hada da ma'aikatan agaji, da masu share-share da masu fasaha, da maiakatan bangaren magunguna da masu aikin lafiyar ido wadanda ke aiki da maiakatar kiwon lafiya ta Kaiser Permanente.

    Yawancin a jihar California suke, amma da wasu da ke jihohin Oregon da Colorado.

    Hakan na zuwa ne bayan babbar kungiyar kula da lafiya mai zaman kanta da kungiyoyin kwadago sun kasa cimma matsaya bayan shafe watanni ana tattaunawa kan albashi, da kuma karancin ma’aikata.

    Likitoci da ma'aikatan jinya da yawa da ke aiki da Kaiser Permanente ba su shiga yajin aikin ba.

  2. An sallami ɗan sanda bisa zargin fyade a Benue

    Rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar Benue ta sallami wani ɗan sanda mai suna Belasa Iyangedue bisa zargin sa da yi wa wata yarinya ‘yar shekara 16 fyade a lokacin da take tsare a ofishin 'yan sanda.

    Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa kwamishinan ‘yan sandan jihar, CP Batholomew Onyeka ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ofishinsa da ke Makurdi.

    Onyeka ya ce rundunar ‘yan sandan Najeriya a matsayinta ta hukuma mai ƙoƙarin tabbatar da ɗa’a ba za ta amince da irin wannan laifin da ya saba wa ka’idojin aikin ba.

    Ya bayyana cewa dan sandan da aka kora ya aikata laifin a ofishin ‘yan sanda na Tse Agbaragba da ke karamar hukumar Konshisha a jihar kuma tuni ya fuskanci hukunci.

    Rahoton da aka samu daga kotun Majistare Makurdi ya bayyana cewa dan sandan ya aikata laifin ne a ranar 16 ga watan Agustan 2023 da misalin karfe 2 na rana.

    A yayin da ake gudanar da bincike bayan an kama Iyangedue, ya amsa laifin da ya aikata wanda ya saɓa wa sashe na 284 na dokokin jihar Binuwai na shekarar 2004.

  3. An zargi jami'an Iran da lakaɗa wa wata yarinya dukan tsiya

    Masu fafutika sun zargi jami'an tabbatar da da'a na Iran da dukan wata yarinya da ba ta sanya hijabi ba har sai da ta suma.

    Armita Geravand, mai shekaru 16, ta fadi ne bayan da ta hau jirgin kasan metro na Tehran a tashar Shohada ranar Lahadi.

    Jami’ai sun ce suma kawai ta yi sannan suka saki bidiyon CCTV inda aka ga an ciro ta a sume daga cikin jirgin.

    Kungiyar kare hakkin bil'adama Hengaw ta yi zargin cewa jami'an 'yan sanda masu kula da da'a sun yi mata "mummunan duka".

    Sanarwar ta ce Armita tana jinya a asibitin Fajr na Tehran bisa tsauraran matakan tsaro, kuma an kwace wayoyin dukkan 'yan uwanta.

    A ranar litinin da ta gabata hukumomi sun tsare wata ‘yar jarida ta jaridar Sharq na takaitaccen lokaci yayin da ta je asibitin domin bayar da rahoto kan lamarin.

    • Bidiyon tsiraici a Iran: Gwamnati ta ce ba ta da matsaniya
    • An gurfanar da mutum 1,000 a kotu kan zanga-zangar Iran
  4. Majalisar Dattijan Najeriya ta tantance ƙarin ministocin Tinubu

    Majalisar dattawan Najeriya a yau Laraba ta kammala tantance wasu ministoci uku da shugaba Bola Tinubu ya gabatar mata.

    An gudanar da zaman tantancewar ne a zauren majalisar da ke Abuja.

    Wadanda aka tantancen su ne: Jamila Bio-Ibrahim daga jihar Kwara da Balarabe Lawal daga Jihar Kaduna da kuma Ayodele Olawande daga jihar Ondo.

    Sai dai a lokacin tantancewar, Balarabe Lawal wanda ya maye gurbin tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya yanke jiki ya fadi, wanda hakan ya sa majalisar ta cigba da zaman a killace bayan ya farfado.

    A ranar 7 ga watan Agusta ne majalisar dattawa ta tabbatar da nadin ministoci 45 daga cikin 48 da Tinubu ya aika.

  5. Moroko za ta karɓi baƙuncin wasannin kofin duniya

    Hukumar kwallon kafa ta duniya, Fifa, ta sanar da cewa Morocco za ta karbi bakuncin wasanni a gasar cin kofin duniya ta maza ta 2030 a wani bangare na karbar bakunci na hadin gwiwa da Sifaniya da Portugal.

    Wannan dai shi ne karo na biyu a tarihin gasar cin kofin duniya da za a gasar a wata ƙasa ta Afirka, bayan da Afirka ta Kudu ta shirya gasar cin kofin duniya a shekarar 2010.

    Uruguay da Argentina da Paraguay ne za su karbi bakuncin wasannin bude gasar domin murnar cika shekaru 100 da fara gasar.

    Yunkurin hadin gwiwa daga Morocco da Portugal da Spain shi ne kadai bukatar karban bakuncin gasar ta 2030. An gudanar da gasar cin kofin duniya ta farko a shekarar 1930 a kasar Uruguay kuma mai masaukin bakin ce ta lashe gasar.

    Wannan shi ne karon farko da za a gudanar da gasar cin kofin duniya a nahiyoyi uku da kasashe shida.

    A wata sanarwa da FIFA ta fitar ta ce "Majalisar FIFA ta amince da cewa bukatar karban bakoncin hadin gwiwar da ta hada da kasashen Morocco da Portugal, da Sifaniya, wadanda za su karbi bakuncin gasar a shekarar 2030 kuma za su samu shiga kai tsaye daga guraben da ake da su."

  6. Gasar kofin duniya 2030: Kasashe 6 za su karbi bakuncin wasannin

  7. An yanke wa ma'aikacin asibiti ɗaurin shekara 35 kan satar yara

    An yanke wa wani ma'aikacin asibiti a Kenya da BBC ta bankaɗo yadda ya nemi sayar da jariri, hukuncin daurin shekaru 35 a gidan yari.

    Fred Leparan, wanda ke aiki a asibitin Mama Lucy Kibaki na Nairobi, an dauki hotonsa a bidiyo yayin da yake karbar dala 2,500 (£2,000) domin sayar da wani jariri da ke karkashin kulawar asibitin.

    Ita ma wadda ake tuhumar su tare, Selina Adundo, wadda ita ma ma’aikaciyar asibiti ce an yanke mata hukuncin daurin shekaru shida a gidan yari ko kuma ta biya tarar dala 2000.

    Fred Leparan zai shafe shekaru 25 a gidan yari, sauran shekaru 10 kuma a tsare a karkashin kulawa ta musamman.

    An kama shi ne a shekarar 2020 bayan wani rahoton sashen binciken ƙwaƙwaf na BBC Africa Eye.

    Ita kuma wadda ake tuhumarsu tare, Selina Adundo an same ta da laifuka uku na rashin kula da yara amma an wanke ta da laifin safarar yara.

    Kotun ta yi gargadin cewa ba za a taba barin dukkansu su gudanar da duk wani lamari da ya shafi yara ba.

    A farkon makon nan Sakatariyar Ma'aikata da Kare Jama'a na Kenya Florence Bore, ta ce gwamnati za ta soke duk wasu gidajen marayu da gidajen yara masu zaman kansu cikin shekaru takwas masu zuwa, matakin da ke da nufin kawo karshen fataucin yara.

  8. An tabbatar da mutuwar mutum 23 a hatsarin jirgin ruwan Kebbi

    Yayin da ake ci gaba da laluɓe, hukumomi sun tabbatar da mutuwar aƙalla mutum 23 sanadiyyar hatsarin jirgin ruwa a ƙaramar hukumar Yauri ta jihar Kebbi.

    An ruwaito cewa mutane da dama ne kuma suka ɓata waɗanda ake ci gaba da nema.

    Waɗanda lamarin ya shafa sun kasance ƴan kasuwa da suka fito daga jihar Neja zuwa Yauri domin cin kasuwa, da ke ci mako-mako.

    Wannan dai ya kasance hatsarin jirgin ruwa na uku da aka samu a ƴan watannin nan, inda wanda ya faru a baya-bayan nan ya janyo mutuwar gwamman mutane.

  9. Kuɗin-cizo sun addabi mazauna babban birnin Faransa

    Al’ummar Paris, babban birnin Faransa da sauran biranen ƙasar na fama da matsalar kuɗin-cizo yayin da ƙasar ke shirye-shiryen ɗaukar baƙuncin gasar guje-guje da tsalle-tsalle ta Olympics.

    Yanzu haka ana ganin irin waɗannan ƙwari a wurare da dama a biranen.

    Sai dai lamarin ya samo asali ne tun daga shekarun da suka gabata.

    Wani masani kan ƙwari, Jean-Michel Berenger ya ce “a ƙarshen lokacin zafi na kowace shekara akan samu ƙaruwar kuɗin-cizo.”

    Ya ƙara da cewa “hakan na faruwa ne saboda mutane da ke yawan tafiye-tafiye a watannin Yuli da Agusta, kuma sukan kwaso su a cikin kayansu.”

    Sai dai a cewarsa “yawan kuɗin-cizon da ake samu na ƙaruwa a kowace shekara.”

    Yanzu haka dai gwamnatin shugaba Emmanuel Macron na buƙatar ganin an ɗauki mataki.

  10. An gurfanar da Naira Marley a gaban kotu kan mutuwar Mohbad

    'Yan sanda a jihar Lagos sun gurfanar da tauraron mawakin Najeriyar nan, Azeez Fashola, wanda kuma ake kira da Naira Marley da takwaransa Balogun Eletu, wanda aka fi sani da suna Sam Larry, game da mutuwar mawaki Ilerioluwa Aloba, wato Mohbad.

    'Yan sanda sun gayyaci Naira Marley da Sam Larry inda suka gurfanar da su a kan kotun majistare da ke Yaba ranar Laraba.

    Jaridar Vanguard ta ambato cewa kotun ta bai wa 'yan sanda damar ci gaba da tsare mutanen biyu don gudanar da bincike.

    Mohbad ya mutu ne ranar 12 ga watan Satumban 2023 a Lagos inda aka binne shi washe gari. Sai dai, wadanda ake zargin sun musanta hannu.

    Mohbad ya bar kungiyar Marlian Records, wadda ke karkashin Naira Marley a kan wata dambarwa da ta kaure bara, sai dai dangantaka tsakanin marigayin da tsohon shugabansa, ta ci gaba da yin tsami har bayan lokacin.

    A lokaci guda kuma, rundunar 'yan sandan Lagos ta ayyana neman Owodunni Ibrahim wanda aka fi sani da Primeboy, a matsayin wanda take nema ruwa a jallo, saboda gazawarsa ta amsa gayyatar da suka yi masa a kan mutuwar Mohbad.

    Wata sanarwar rundunar da wani mai magana da yawun 'yan sandan Lagos, SP Benjamin Hundeyin ya fitar a ranar Laraba, ta ce sun dauki matakin ne saboda gazawar Primeboy ta amsa goron gayyatar da aka aika masa tun bayan fara bincike cikin wannan lamari da ya kai ga mutuwar Mohbad.

    Kwamishinan 'yan sandan Lagos, CP Idowu Owohunwa ya yi alkawarin bayar da ladan naira miliyan daya ga duk wanda yake da bayani mai amfani da zai kai ga kama Primeboy.

  11. Klopp ya buƙaci a sake buga wasan Liverpool da Tottenham

  12. Wani hari ya lalata ofishin jakadancin Habasha a Sudan

    Wani babban jami'in kasar Habasha ya tabbatar da kai hari ofishin jakadancin ƙasar da ke Khartoum, babban birnin Sudan.

    Ba a samu asarar rai ba sakamakon harin na ranar Talata, amma ofishin jakadanci ya samu rauni a wani bangare, kamar yadda Yibeltal Ayimiro Alemu, jakadan Habasha a Sudan, ya shaida wa BBC.

    Rundunar 'yan sandan ƙasar Sudan ta RSF, wacce ke fafatawa da sojoji tun ranar 15 ga watan Afrilu, ta zargi sojoji da kai harin.

    Sojojin Sudan ba su ce komai ba.

    Wannan dai ba shi ne karon farko da aka kai wa ofishin jakadancin Habasha da ke Khartoum hari ba.

    Wani ma'aikacin ofishin jakadancin Habasha da ke Sudan ya shaida wa BBC cewa an kai wa ofishin hari ta sama makonni uku da suka wuce.

    Jami’in ya ce jami’an tsaro sun samu raunuka tare da farfasa tagogi.

    Sama da mutum 5,000 ne suka mutu a rikicin, yayin da wasu miliyan biyar suka rasa matsugunansu, a cewar MDD.

  13. 'Muna bincike kan zargin rashin bai wa sojojinmu isasshen abinci'

  14. An kai yara asibiti bayan sun sha alewar da aka yi da wiwi

    An kai yara sama da 60 asibiti a Jamaica bayan sun sha alewar da aka yi da tabar wiwi, in ji ministan ilimi na ƙasar.

    Fayval Williams ta rubuta a kan shafinta na X cewa ɗaliban firamaren sun fito ne daga yankin St Ann's Bay, kimanin kilomita 80 daga Kingston, babban birnin ƙasar.

    Ta ce wasu daga cikin yaran sun yi ta yin amai da mafarkin-zaune, inda ta ƙara da cewa babu wani yaro da aka ruwaito yana cikin mummunan yanayi.

    "Likitoci da ma'aikatan jinya suna yin duk abin da za su iya don tabbatar da cewa ɗaliban sun murmure," in ji Williams.

    Ana kyautata zaton cewa yaran suna tsakanin shekaru 12 zuwa ƙasa.

    Shugaban makarantar ya shaida wa jaridar Jamaica Observer cewa wani "mai sayar da alawa ne ya sayar wa da ɗaliban alawar.

    Shugaban sashen ‘yan sanda na St Ann, Dwight Powell, ya buƙaci wanda ke da bayanai game da shi da ya tuntuɓi hukuma.

    • WHO tana ganin wani maganin tari ne ya kashe yara 66 a Gambiya
    • Africa Eye Kush: Yadda tabar wiwi take haukata matasa a Sierra Leone
  15. Amurka ta kakaba wa kamfanonin China takunkumi

    Amurka, ta ba da sanarwar sanya takunkumi kan wasu mutane da kuma hukumomin China da dama don samarwa da rarraba wasu sinadarai da ake amfani da su wajen samar da maganin nan na Fentanyl da ake amfani da shi wajen rage raɗaɗi.

    Ma'aikatar shari'a ta Amurka ta kuma sanar da tuhume-tuhume kan wasu kamfanoni da ma'aikatan da ke samar da sinadarai na ƙasar ta China.

    An yi imanin cewa Fentanyl ya kashe dubban mutane a Amurka saboda yadda suke masa shan wuce ka'ida.

    Babban mai shigar da kara na Amurka Merrick Garland ya ce, sun gano cewa ana sarrafa maganin ne a Mexico ta hanyar amfani da kayayyaki daga China kafin a yi safarar su cikin Amurka ta hanyar wasu 'yan kasuwa.

    • Amurka ta sanya wa 'yan Hisbah takunkumi a Iran
    • Ko China za ta iya kere Amurka a fagen ƙirƙirarriyar basira ta AI?
  16. Ministan da Tinubu ya tura wa majalisa ya faɗi a lokacin tantancewa

    Ɗaya daga cikin ministocin da shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura wa Majalisar dokokin ƙasar domin tantancewa ya yanke jiki ya faɗi a zauren majalisar.

    Ministan wanda ya fito daga jihar Kaduna, Balarabe Abbas Lawal ya faɗi ne a daidai lokacin da ya kammala jawabi kan tarihin rayuwa da karatunsa.

    Sai dai nan da nan aka ɗaga shi kuma aka zaunar da shi a kan kujera.

    Majalisar dai ta shiga zaman sirri bayan faɗuwar sa.

    Tun farko a lokacin da yake jawabi, Abbas ya shaida wa majalisar cewa ya yi matuƙar murnar damar da ya samu, kuma yanayi ne da bai taɓa tsintar kansa a ciki ba.

  17. Majalisar dattawa tana tantance karin ministocin Tinubu uku

    Majalisar dattawa ta ci gaba da zama a yau Laraba don tantance sabbin ministoci uku da Shugaba Bola Tinubu ya aika mata don neman amincewa.

    Wadanda ake tantancewar sun hada da Balarabe Abbas Lawal daga jihar Kaduna da Dr Jamila Bio Ibrahim daga jihar Kwara da kuma Ayodele Olawande daga jihar Ondo.

    A ranar Talata ne shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya karanta wasikar da shugaba Tinubu ya aika wa 'yan majalisar inda ya bukaci ta amince da karin wasu ministoci guda uku.

    Majalisar dattijai dai a watan Agustan 2023, ta tantance tare da tabbatar da ministoci 45, amma ta yi watsi da mutum uku a cikinsu.

    Daga cikin wadanda ba ta tabbatar da su ba, akwai tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai da Stella Okotete daga jihar Delta da kuma Abubakar Danladi daga jihar Taraba.

    • Majalisar Dattijai ta fara tantance ministoci a Najeriya
    • Abin da ya yi wa El-Rufai cikas wajen tabbatar da shi ministan Tinubu
  18. Jirgin ruwa dauke da 'yan ci-rani 280 ya isa tsibirin Canary

    Wani ƙaramin jirgin ruwa dauke da bakin haure 280 ya isa tsibirin Canary na kasar Sifaniya.

    Jirgin ya isa tsibirin El Hierro mai nisan kilomita 380 daga gabar tekun Afirka ta Yamma a ranar Talata.

    Masu aikin ceto sun ce wadanda ke cikin jirgin ‘yan asalin yankin kudu da hamadar Sahara ne kuma shi ne mafi yawan bakin haure da suka isa tsibirin a tashi guda.

    Tsallakawa zuwa tsibirin Canary, na ɗaya daga cikin hanyoyin da bakin haure suka fi amfani da su kuma masu hatsari zuwa Turai daga Afirka.

    Tun a farkon shekarar nan, mutum 140 ne suka mutu ko kuma suka bata a lokacin da suka yunkurin tsallakawa, a cewar Hukumar Kula da Hijira ta Duniya.

    Amfani da hanyar ya karu a 'yan shekarun nan, yayin da aka tsaurara matakan dakile mutanen da ke tsallakawa tekun Bahar Rum daga gabar tekun Afirka ta Yamma.

    Tsakanin 1 ga watan Janairu zuwa 30 ga watan Satumban bana, jimillar bakin haure 14,976 ne suka isa tsibirin Canary, wanda ya karu da kashi sama 19 cikin 100 a daidai wannan lokaci a shekarar 2022, a cewar alkaluman ma'aikatar harkokin cikin gida ta Sifaniya.

    A ranar Lahadin da ta gabata ne, sojojin ruwan Senegal suka ce sun kama wasu jiragen ruwa guda hudu cikin kwana uku dauke da 'yan ci-rani sama da 600.

    • ‘Yadda muka maƙale a tsakiyar teku bayan man jirgi ya ƙare’
    • La Palma: Aman wuta ya laƙume gidaje sama da 200 a Spain
  19. An yi jana'izar dattijuwar Kannywood, Binta Ola Katsina

    Dangi da 'yan'uwa har ma da abokan arziki na ci gaba da mika sakonnin ta'aziyya da kuma alhini, bisa rasuwar fitacciyar 'yar Kannywood kuma mai wasannin kwaikwayo, Binta Ola Katsina.

    Ta rasu ne bayan wata gajeriyar jinya cikin daren Laraba a gidanta da ke cikin birnin Katsina.

    Binta Ola ta shafe tsawon shekaru tana gudanar da wasannin kwaikwayo ciki har da wasannin daɓe da na rediyo, kafin ta fara bayyana a fina-finan masana'antar Kannywood daga bisani.

    Bayanan da BBC ta samu sun ce dattijuwar ta kammala shirye-shirye don bikin Mauludi wayewar garin Laraba, amma sai ta kamu da rashin lafiya cikin tsakiyar dare, kafin rasuwarta.

    Wani fim da ya kara fito da ita a baya-bayan nan shi ne shirin talbijin mai dogon zango na Dadin Kowa.

    Dangin marigayiyar sun ce ba su tabbaci kan ainihin shekarunta a duniya.

  20. Yawan sojojin Nijar da aka kashe a harin Tillaberi ya ƙaru zuwa 60