Tattalin arziƙin manyan ƙasashen Afirka na tafiyar hawainiya mafi muni a tarihi
Wani sabon rahoto da hukumar kula da harkokin tattalin arziki ta McKinsey ta fitar ya nuna cewa, manyan kasashen Afirka da suka fi girman tattalin arziki da suka hada da Afirka ta Kudu da Masar da Najeriya da kuma Aljeriya suna samun ci gaba mafi kankanta a nahiyar.
"Habakar da aka samu a baya ta samo asali ne ta hanyar albarkatu." A cewar Acha Leke wani babban jami'i a McKinsey.
Rahoton ya nuna cewa, yadda wadannan kasashe ke gudanar da tattalin arzikinsu, ya jawo koma-baya ga ci gaban nahiyar baki daya.
"Idan aka yi la'akari da ci gaban da aka samu cikin shekaru 10, an samu karuwa da kashi 3.3% wanda ba shi da armashi idan aka dubi karuwar yawan jama'a. Amma akwai manyan bambance-bambance a cikin Afirka."
Rahoton ya kara da cewa kasashen da ke kan gaba wajen bunkasar tattalin arzikin nahiyar a ko da yaushe, su ne kasashen gabashin Afirka musamman kasar Rwanda. A baya-bayan nan, wasu kasashe a yammacin Afirka, kamar Ivory Coast, sun sami karuwar ci gaba.
Sakamakon haka, Mista Leke ya ce nan gaba, ci gaban zai ta'allaka ne kan karfafa kasuwanci tsakanin yankuna, da taimaka wa harkokin kasuwancin Afirka wajen habaka, da kuma inganta ma'aikata.