Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Aisha Buhari ta janye ƙarar da ta kai ɗalibi Aminu Muhammad, in ji lauyansa

Wannan shafi na kawo maku labaran abubuwan da suke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi and Umar Mikail

  1. Ƙarshen rahotannin ke nan

    Masu bibiyarmu a wannan shafi, ƙarshen rahotannin ke nan na yau Juma'a.

    Ku tara gobe da safe don samun wasu rahotannin kai-tsaye a wani shafin daban.

    Kafin lokacin, ku duba ƙasa don karanta abubuwan da muka wallafa.

    Mu kwana lafiya.

  2. Rasha ta yi watsi da tayin tattaunawa tsakanin Putin da Biden

    Fadar Kremlin ta Shugaba Putin na Rasha ta yi watsi da kalaman Shugaban Amurka Joe Biden cewa a shirye yake ya tattauna da Putin ɗin idan har yana son kawo ƙarshen yakin Ukraine.

    Mista Biden ya jaddada cewa haka na iya faruwa ne kawai idan sojojin Rasha suka janye daga Ukraine.

    Kakakin Kremlin Dmitry Peskov ya ce Rasha ba ta shirya cika waɗan nan ƙa’idojin ba.

    A hirarsu ta waya da shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz, Mista Putin ya bayyana halayyar da ƙasashen Yamma ke nunawa ga Ukraine a matsayin ɓarna.

    Ya kuma ya ce ba lalle a je teburin sulhu ba yayin da ƙasashen na Yamma ke bai wa Ukraine dukkanin goyon baya ta fuskar siyasa da kuma kuɗaɗe.

  3. Yawan matan da ke mutuwa yayin haihuwa a Afirka ya ƙaru - WHO

    Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ja hankalin duniya kan koma-bayan da ake samu na mace-macen mata masu ciki da ƙananan yara a ƙasashen Afirka.

    Wani rahoto da hukumar ta fitar jiya Alhamis ya yi hasashen cewa mata 390 ne za su dinga mutuwa yayin da suke ƙoƙarin haihuwa a dukkan haihuwa 100,000.

    Rahoton ya kuma ce wannan adadin ya ninka mizanin da aka shirya cimma wa har sau biyar daga yanzu zuwa 2030,.

    Ku danna hoton ƙasa don sauraron rahoton da Sani Aliyu ya haɗa daga Abuja:

  4. IGP Usman Baba na neman kotu ta jingine hukuncin da ya ɗaure shi wata uku

    Sufeto Janar na 'Yan Sandan Najeriya IGP Usman Alkali Baba ya shigar da ƙudirin neman jingine umarnin kotun da ya ɗaure shi wata uku a gidan yari, yana mai cewa bai raina umarnin kotun ba.

    Cikin ƙorafin da ya gabatar a gaban Babbar Kotun Tarayya a Abuja ranar Alhamis, shugaban 'yan sandan ya ce ba a ƙarƙashin shugabancinsa aka aikata laifin da kotun ta yi hukunci a kansa ba kuma "ba a saɓa wa umarnin kotu ba".

    A makon nan ne Babbar Kotun Tarayya ta ba da umarnin kama babban sufeton tare da garƙame shi tsawon wata uku saboda saɓa umarnin kotun da ta ce a mayar da Patrick C. Okoli kan aikinsa bayan an tilasta masa yin ritaya ba bisa ƙa'ida ba.

    "Ya tabbatar da cewa an ba da umarnin ne a Nuwamban 2018 da kuma Janairun 2019 ga sufeto janar na 'yan sanda na lokacin, ba a kansa ba wanda shi ne yake riƙe da muƙamin a yanzu," a cewar wata sanarwa da rundunar ta fitar a yau Juma'a.

    IGP Usman Baba ya ƙara da cewa sufeto janar na lokacin ya bi umarnin kotun, inda ya rubuta wasiƙa ga hukumar kula da harkokin 'ya sanda don a mayar da Mista Okoli bakin aiki.

    Sai dai sanarwar ba ta bayyana dalilin da ya sa rundunar ta gaza mayar da shi bakin aiki ba kafin kotun ta ba da umarnin kama shugaban nata a ranar Talata da ta gabata.

    Karanta ƙarin bayani:

    • Dalilin da ya sa ba a kama shugaban EFCC da na 'yan sanda ba duk da umarnin kotu
  5. An samu ƙararrakin cin zarafin mata da yara 4,000 a Legas cikin 2022

    Kwamashina a maa'aikatar harkokin mata da yaƙi da fatara a Najeriya, Cecilia Bolaji Dada, ta bayyana cewa an samu ƙararraki na cin zarafin mata har 4,351 a Jihar Legas a tsakanin watan Janairu zuwa Nuwamban 2022.

    Ta bayyana haka a wani taron manema labarai da aka shirya tare da haɗin gwiwar asusun kula da yawan jama'a na Majalisar Ɗinkin Ɗuniya (UNFPA) don ba da sanarwar ayyukansu na shekara ta 2022.

    Ƙarƙashin jagorancin Cecilia Dada, za a shafe kwana 16 ana gudanar da gangami don neman kare haƙƙoƙin mata da yara.

    Sukan gudanar da gangamin shekara-shekara daga kowace ranar 25 ga watan Nuwamba har zuwa 10 ga watan Disamba.

    Danna hoton da ke ƙasa ku saurari rahoton wakilinmu Umar Shehu Elleman daga Legas:

  6. Ukraine za ta dakatar da ƙungiyoyin addini masu taimaka wa Rasha

    Shugaban Ukraine, Volodymyr Zelensky, ya ce zai tabbatar da ƴancin ƙasarsa yayin da ya sanar da ƙudirin haramta wa ƙungiyoyin addini da ke da alaƙa da Rasha gudanar da harkokinsu a Ukraine.

    Ya yi alƙawarin jami’an tsaron Ukraine za su tsaurara matakan yaƙi da ayyukan masu zagon ƙasa, waɗanda ya yi zargin jami’an leƙen asirin Rasha na aiwatarwa da sunan ƙungiyoyin addinin.

    Hukumomin Ukraine sun gudanar da bincike a baya-bayan nan kan wuraren da wani reshen cocin Orthodox ke tafiyar da su da sai a baya-bayan nan ya nuna mubaya’a ga cocin orthodox na Rasha.

    Zelensky ya ce dole ƙasar ta bijiro da ƙa’idoji domin kada wani da ke dogaro da Rasha ya yi amfani da ƴan Ukraine tare da raunana ƙasar.

  7. Labarai da dumi-dumi, Qatar 2022: Ghana ta kasa kaiwa zagaye na gaba a Kofin Duniya

    An kori tawagar ƙwallon ƙafa ta Ghana daga Gasar Kofin Duniya bayan Uruguay ta doke ta 0-2 a wasan ƙarshe na Rukunin H.

    Ɗan wasan Ghana kuma kaftin ɗin tawagar ya kasa cin bugun finaretin da aka ba su bayan mai tsaron raga Rochet ya bigi ƙafar Kudus. Shi ne dai kuma ya kaɗe ƙwallon da Ayew ya buga masa a minti na 21.

    Sai dai ita ma Uruguay ta fita daga gasar duk da nasarar da ta samu saboda ƙwallo biyu kawai ta zira a raga idan aka kwatanta da na Koriya ta Kudu huɗu.

    Portugal da Koriya ne suka tsallaka zagayen 'yan 16 daga rukunin.

    Ghana ta ƙare wasan a ƙasan teburi da maki uku, yayin da Portugal ta kasance ta ɗaya da maki shida, sai Koriya mai maki huɗu bayan ta doke Portugal ɗin da 2-1.

  8. Labarai da dumi-dumi, Aisha Buhari ta janye ƙarar da ta kai ɗalibi Aminu Muhammad, in ji lauyansa

    Matar Shugaban Najeriya Aisha Buhari ta janye ƙara da kuma tuhumar da take yi wa ɗalibin nan Aminu Muhammad, kamar yadda lauyansa ya shaida wa BBC Hausa.

    Cikin wani saƙon tes, Barista C.K. Agu bai yi ƙarin bayani ba game da dalilin da ya sa Aisha ta janye ƙarar.

    Matakin na zuwa ne bayan ɗalibin, wanda ke karatu a Jami'ar Tarayya da ke Dutse, ya shafe kwana uku a gidan yari da ke Suleja bisa umarnin kotun bayan ya ƙi amsa laifinsa.

    A ranar Litinin ake sa ran ci gaba da zaman kotun don sauraron neman beli da lauyan Aminu ya yi a zaman ranar Talata da aka yi, wanda bai yi nasara ba.

    Matar shugaban na zargin Aminu da ɓata mata suna saboda saƙon da ya wallafa a shafinsa na Twitter maƙale da hotonta tare da cewa "ta ci kuɗin talakawa".

    Ƙungiyoyin kare haƙƙi da masu sharhi sun soki Aisha game da matakin da ta ɗauka bayan rahotanni sun yi zargin cewa sai da aka lakaɗa wa Aminu duka kafin gurfanar da shi a gaban kotun.

    Kazalika, wasu sun soki matashin kan zargin da ya yi wa matar shugaban.

    • Tarihin ɗalibin da ake zargin Aisha Buhari ta 'tsare' kan cin zarafinta
  9. Shugaban ƙasar Kenya ya kori jami'an hukumar zaɓen ƙasar

    Shugaban ƙasar Kenya William Ruto ya dakatar da wasu Kwamishinonin hukumar zaɓe ta ƙasar su huɗu, waɗanda suka ƙi sanya hannu kan sakamakon zaɓen ƙasar wanda ya ba shi nasara.

    Mr Ruto ya sanara a yau Juma'a cewar an samar da wani kwamiti wanda zai binciki jami'an huɗu bisa zargin su da taka doka, da rashin ƙwarewa wurin aiki, wani abu da ka iya sanadiyyar koran su daga aiki.

    Sai dai jagoran ƴan adawa na ƙasar Raila Odinga ya soki matakin shugaban ƙasar, inda ya bayyana shi a matsayin wani mataki na shirin yin maguɗi a zaɓen ƙasar na 2027.

    Korar da shugaban ya yi wa jami'an hukumar zaɓen ta zo ne bayan shawarar da majlisar dokokin ƙasar ta bayar na dakatar da su saboda abin da suka aikata a lokacin zaɓen ƙasar na watan Agusta.

    Mr Ruto ne ya yi nasara a zaɓen bayan ya yi nasara da ƙaramin rinjaye a kan ɗan takara na jam'iyyar adawa Raila Odinga.

  10. Wani jagoran siyasar Afghanistan ya tsallake rijiya da baya a hare-haren ƙunar baƙin wake

    Magoya bayan jagoran siyasa a Afghanistan, Gulbuddin Hekmatyar, sun ce ya tsallake rijiya da baya bayan wasu hare-haren ƙunar baƙin wake da aka kai kan ofishinsa da ke Kabul.

    Rahotanni na cewa an harbe maharan kafin su kutsa cikin ginin.

    Wasu masu gadi biyu kuma sun ji rauni sanadiyyar fashewar.

    Jami’an Taliban sun killace wajen kuma zuwa yanzu, babu wata ƙungiya da ta ɗauki nauyin kai harin.

  11. Dakarun Najeriya sun kashe mayaƙan Boko Haram da dama a Borno

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta sun samu gagarumin nasara a wani farmaki da suka kai ranar Alhamis kan sansanonin mayaƙan ƙungiyar Boko Haram a jihar Borno.

    Sanarwar da rundunar ta wallafa a shafinta na sada zumunta ya ce dakarun na Operation Hadin Kai sun kai harin ne a wani yanki da ke kan hanyar Wajiroko zuwa Damboa, wanda ya zarce zuwa Maiduguri.

    A lokacin harin, sanarwar ta ce an hallaka mayaƙan ƙungiyar Boko Haram da na ISWAP da dama.

    Haka nan dakarun sun ƙwato bindigogi da harsasai, da motoci da kuma kayan yaƙi da dama.

  12. Satar amsa lokacin jarrabawa babbar matsala ce a Najeriya - Ministan Ilimi

    Ministan ilimi na Najeriya Adamu Adamu ya buƙaci hukumomin shirya jarrabawa a Najeriya da su yi amfani da fasahar zamani wajen magance matsalar satar amsa lokacin jarrabawa.

    Ministan ya bayyana haka ne a lokacin buɗe taron tattaunawa kan yadda za a magance satar amsa, wanda majalisar dokokin Najeriya da hukumar shirya jarrabawa ta ƙasa (NECO) suka shirya a Legas.

    Adamu ya ce “satar amsa lokacin jarrabawa babbar matsala ce da ke illa ga yadda hukumomi ke shirya jarrabawa a Najeriya.”

    Ya ce Najeriya ƙasa ce da take baya a harkar magance satar amsa.

    Ya ƙara da cewa ya zama wajibi a yi amfani da fasahar zamani wajen ganin an tsaftace harkar jarrabawa ta ƙasar.

  13. An kama yara biyu bisa zargin kisan wasu yara biyu a London

    An gurfanar da wasu yara biyu bisa zargin su da amfani da wuƙa wajen kashe wasu yaran biyu a kudu maso gabashin birnin London.

    Yaro na farko da aka kashe, Kearne Solanke ɗan shekara 16, an same shi ne da munanan raunuka ranar Asabar a yankin Thamesmead.

    Shi kuma Charlie Bartolo ɗan shekara 16 an same shi ne a Abbey Wood duk a rana guda.

    Mai magana da yawun rundunar ƴansandan London ya ce duk yunƙurin da masu kai ɗaukin gaggawa suka yi, yaran biyu sun rasu.

    Ana sa ran bayyanar yaran biyu masu shekaru 15 da 16 da ake zargi a gaban kotu nan gaba kaɗan.

    Yanzu haka dai ɓangaren kula da manyan laifuka na ƴan sanda na ci gaba da bincike kan lamarin.

  14. Obasanjo ya ce tasirin Najeriya na raguwa a idon duniya, Daga Ibrahim Isa a Abuja

    Masana harkokin dfplomasiyya a Najeriya, sun fara tofa albarkacin bakinsu a kan wani furuci da tsohon shugaban kasar, Cif Olusegun Obasanjo ya yi cewa tasirin Najeriya a duniya yana raguwa, musamman ma a kan kasashen nahiyar Afirka.

    Wasu masana na ganin cewa akwai gaskiya a cikin maganar, suna danganta lamarin da rashin ƙwararrun masu ba da shawara ga shugabanni da kuma rashin aiki da ita idan an ba su.

    Tsohon shugaban Najeriya Cif Olusegun Obasanjo, ya yi wannan furucin ne a wajen wani bikin ƙaddamar da littafi a kansa, musamman ma yadda ya shahara wajen rubuta wa shugabannin Najeriya wasikar bankada ko tonun silili.

    Ya ce tasirin kasar na fada a ji da kuma dadadden kallon da ake mata na babbar Yaya, kuma rumfa sha shirgi na ci gaba da raguwa musamman ma a kan kasashen nahiyar Afirka, sakamakon gazawa ko rashin tabuka abin kirki wajen jagorantar kannen nata.

    Cif Obasanjon ya buga misali da wata gazawa da ya ce Najeriya ta yi wajen daidaita tsakanin shugabanni da ƴan tawaye a kasar Chadi - lamarin da sai da ƙasar Qatar ta dako gari daga nahiyar Asiya ta je ta shiga tsakani.

    Tuni dai wasu masana huldar jakadanci suka fara tofa nasu albarkacin bakin a kan wannan maganar.

    Ambasada Sulaiman Dahiru, tsohon jakadan Najeriya ne, wanda ya ce duk da cewa Cif Obasanjo kan ji babu wanda ya yi komai in ba shi ba…a wannan ɓigiren ya fadi gaskiya.

    Sai dai na tambayi Ambasada Sulaiman Dahiru ko da wani abu da Najeriyar za ta yi don mai da martabar tata ta jagora ga kasashen nahiyar Afirkan?

    A shekarun baya, an yi zamanin da Najeriya ta yi tasiri a kan kasashen Afirka da wasu kasashen duniya, musamman irin rawar da ta taka wajen yaki da nuna launin fata a kasar Afirka ta kudu da wasu makwabtanta.

    Akwai ma lokacin da kasa irin Amurka ba ta daukar wani mataki a kan Afirka sai ta nemi shawarar Najeriya.

  15. An soke shirin yin gwanjon ƙoƙon kawunan wasu ƴan Afirka a Belgium

    An tursasa wani gidan sayar da kaya da ke Belgium soke shirinsa na sayar da ƙoƙon kawuna uku na wasu ƴan Afirka da aka kashe lokacin mulkin mallaka a yankin da yanzu yake cikin Jamhuriyar Demokuraɗiyyar Congo.

    Kantin yin gwanjon kaya na Vanderkindere da ke Brussels ne ya shirya yin holin ƙoƙunan kan mutanen, waɗanda aka kashe tsakanin shekarun 1893 da 1894.

    Lamarin ya fusata mutane da dama a ƙasar, inda masu kare haƙƙin bil'adama suka bayyana lamarin a matsayin cin mutunci da kuma wariyar launin fata.

    Ƙungiyoyi sun yi kira da a yi zanga-zangar nuna adawa da baje-kolin ƙoƙunan kan, tare da kira ga hukumomi da su ƙwace tare da adana ƙoƙunan cikin mutunci.

    A yanzu kantin yin gwanjon ya soke shirin nasa, sannan ya nemi afuwa ga mutanen da ba su ji daɗin shirin nasa ba.

  16. An buƙaci masallatai da coci-coci su rage hargowa cikin dare a Nairobi

    An buƙaci masallatai da coci-coci a birnin Nairobi na ƙasar Kenya da su rage hayaniyar da masu ibada ke yi a cikinsu.

    A wani sako ta shafinsa na tuwita, gwamnan Nairobi, Johnson Sakaja ya ce zai tattauna da jagororin addini kan yadda za a rage hargowar da ke fitowa daga wuraren ibadar.

    A kwanan nan ne hukumomin birnin suka haramta samar da wuraren shakatawar dare a unguwannin al'umma saboda yawan hayaniya, a yanzu wasu mutanen na kiraye-kirayen ganin an aiwatar da irin wannan doka a kan wuraren ibada.

    Gabanin wallafa bayanin nasa, a ranar Alhamis gwamnan ya ce ba zai bayar da umurnin rufe wuraren ibadan ba, amma zai yi ƙoƙarin tattaunawa da jagororin addinan.

    Nairobi, birni ne da ke da yawan coci-coci waɗanda suka yi ƙaurin suna wurin hargowa a lokacin ibada cikin dare.

  17. Ana cin zarafin yara fiye da kowa a Kano - NHRC

    Ofishin Hukumar kare haƙƙin bil’adama ta Najeriya a jihar Kano ya ce ya samu rahoton cin zarafi mai nasaba da jinsi guda 1,300 daga watan Janairu zuwa Oktoba na shekarar 2022.

    Kuma a cewar shugaban ofishin, Shehu Abdullahi, ƙananan yara ƴan ƙasa da shekara tara ne suka fi fuskantar cin zarafin, haka nan lamarin ya kai ga mutuwar wasu daga cikin su da kuma haifar da lalurar ƙwaƙwalwa.

    Abdullahi ya bayyana haka ne a wani taron da aka gudanar domin tunawa da ranar masu fafutika ta duniya, ta shekarar 2022.

    Jami’in ya ce ya zama wajibi a haɗa hannu tsakanin masu ruwa da tsaki domin kawar da matsalar.

  18. An murƙushe barazanar juyin mulki a Burkina Faso

    Shugaban gwamnatin riƙon ƙwarya ta Burkina Faso, kyaftin Ibrahim Traoré, ya sanar da cewa an yi ƙoƙarin halaka shi a wani yunƙurin juyin mulki a makon jiya.

    A wata tattaunawa da ƙungiyoyin farar hula a jiya Alhamis, Traore ya tabbatar da yunƙurin yi masa juyin mulkin, kuma ya ce ya san waɗanda suka kitsa shi, sai dai ya ce ba zai kama kowa ba saboda ya fi son a bi hanyoyi na tattaunawa.

    Kuma ya tabbatar da cewa a yanzu lamurra sun daidaita.

    A ranar 30 ga watan Satumba ne kyaftin Taraore ya hau kan mulki bayan tuntsurar da gwamnatin laftanar kanar Paul-Henri Damiba.

  19. Indonesia za ta tsaurara hukunci kan mazinata

    Majalisar dokokin Indonesia na shirin amincewa da wata doka ta hukunta mazinata, inda za a iya ɗaure mutum tsawon shekara guda idan aka same shi da laifi.

    Sabbin dokokin za su ƙunshi dokar da za ta haramta cin fuskar shugaban ƙasa ko gwamnati, da kuma bayyana ra’ayin da ya ci karo da muradan ƙasar.

    Haka nan ana haramta zamantakewar namiji da mace ba tare da aure ba..

    Ƙaramin ministan shari’a na ƙasar ya shaida wa Reuters cewa a ranar 15 ga watan Disamba ne ake sa ran majalisar za ta amince da sabbin dokokin, bayan kwashe shekaru ana aiki a kansu.

  20. Yawan mutanen da ke rasuwa sanadiyyar HIV a Najeriya sun ragu

    Sakataren gwamanatin tarayyar Najeriya Boss Mustapha ya ce mutanen da ke mutuwa sanadiyyar cuta mai karya garkuwar jiki sun ragu a ƙasar.

    A lokacin taron tunawa da ranar yaƙi da cutar AIDS ta duniya, wanda ya gudana ranar Alhamis a Abuja, Mustapha ya ce mace-mace sun ragu daga 264,463 a 2015 zuwa 51,000 a bana.

    Haka nan ya bayyana cewa an kuma samu raguwa a yawan mutanen da ke kamuwa da cutar.

    Sakataren na gwamnatin tarayya ya buƙaci majalisun dokokin jihohi su amince da dokar haramta tsangwamar masu cutar HIV domin ɗorewar nasarar da ake samu wurin yaƙi da cutar.