Malaman addinin Islama shida sun rasa rayukansu a mummunan hadarin mota a Kano
Wani mummunan hadarin mota yayi sanadin mutuwar wasu malaman addinin Islama shida a jihar Kano a yau Laraba.
Malaman sun rasu ne a kan hanyarsu ta komawa Kano daga karamar hukumar Sumaila bayan sun kammala aikin da'awah a karkashin gidaunyar Imam Malik.
Wata ma'aikaciyar gidauniyar ta shaida ma jaridar Daily Nigerian cewa da misalin karfe 3 na yammaci suka sami labarin hadarin.
Ta ce hadarin ya rutsa da dukkan malamai shida, wadanda jagororin aikin da'awa ne na gidauniyar.
Sai dai hukumar kiyaye hadurra, FRSC ta ce ba a sanar da ita aukuwar hadarin ba, amma kakakin hukumar ya shaida wa jaridar ta Daily Nigerian cewa za su gudanar da bincike.