Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Firaministan Isra'ila ya fusata bayan wani Bafalasdine ya kashe Yahudawa uku

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Afirka da sauran sassan duniya musamman Ukraine da Rasha.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Mayaƙan I-S sun kashe sojojin Burkina Faso 12 yayin wani hari

    Rundunar sojin Burkina Faso ta ce wasu mahara da ake alakantawa da kungiyoyin jihadin sun halaka akalla sojojinta 12 tare da wasu 'yan sa-kai hudu a wani hari da aka kai kan wani sansanin sojoji.

    Rundunar ta kuma ce an raunata wasu sojojin 21 yayin harin wanda aka kai kan sansanin Namissiguima a arewacin kasar.

    A watan jiya ma akalla sojoji 10 aka kashe a yankin gabashin Burkina Faso.

    Mayakan kungiyoyin da ke ikirarin jihadi sun fara kai hare-hare a Burkina Faso ne a 2015 daga sansanoninsu da ke kasar Mali mai makwabtaka.

  2. Tarayyar Turai ta yi ma Ukraine tayin shiga kungiyar cikin hanzari

    Tarayyar Turai ta mika wa Shugaba Zelensky wata takarda cike da tambayoyi wadda za ta iya ba Ukraine damar zama mambar Tarayyar Turai ta hanyar ba ta mukami na musamman na kasashen da ke daf da zama mambobin kungiyar.

    Yayin da take magana da shugaban na Ukraine, shugabar hukumar gudanarwa ta hukumar, Ursula von der Leyen ta ce Tarayyar Turai za ta goyi bayan Ukraine domin ta kammala bukatun shiga kungiyar "cikin makonni, ba shekaru ba", domin an hanzarta lamarin saboda yakin da ke faruwa.

    Shugaba Zelensky ya tabbatar wa 'yan jarida cewa za a cika bukatun da ke ckin takardar nan da mako guda.

  3. Firaministan Isra'ila ya fusata bayan wani Bafalasdine ya kashe Yahudawa uku

    Firaministan Isra'ila Naftali Bennett ya ce za a ba jami'an tsaron kasar "cikakken 'yanci" domin magance matsalolin tsaro bayn harin da aka kai wanda ya halak wasu Isra'ilawa uku.

    An dai kashe mutum biyu ne yayin da wani Bafalasdine ya bude wuta a wata mashaya a daren Alhamis. Na ukunsu ya mutu ranar Juma'a.

    Maharin ya tsere kuma an shafe sa'o'i jami'an tsaro na farautarsa kafin daga baya suka harbe shi.

    Mahara sun sa Isra;ila a gaba, inda kawo yanzu sun hallaka 'yan kasar 14.

  4. 'Ka cika hassada' - Ronaldo ya mayar wa Rooney martani

    Shahararren dan wasan kwallon kafa Cristiano Ronaldo ya mayar wa tsohon abokin wasansa na kwallon kafa, Wayne Rooney martani kan kalaman da ya furta cewa Ronaldo ya yi kuskuren komawa tsohuwar kungiyar Manchester United.

    Tun da fari, Rooney ya ce a ganinsa Ronaldo ya "fara tsufa" kuma ya ce "ya rage kuzari, ba kamar yadda aka san shi a da ba", inda tsohon dan wasan kungiyoyin Juventus da Real Madrid ya rika shan suka daga 'yan kallo saboda gazawar da yayi na cin kwallo kamar yadda kungiyar United ke bukata a yanzu.

    A martanin da ya mayar a Instagram, Ronaldo ya ce tsohon abokin wasan nasa "ya cika hassada".

    Sai dai duk da ana sukarsa, Ronaldo ya ci kwallaye 18 a wasanni 32 da ya buga a kakar wasan kwallon kafa ta bana.

  5. Rasha ta musanta kai harin tashar jirgin ƙasa da ya kashe mutum 40

    Gwamnatin Rasha ta musanta kai harin roka kan tashar jirgin ƙasa ta Kramatorsk a Ukraine, wanda ya hukumomi suka ce ya halaka mutum 40 zuwa yanzu ciki har da ƙananan yara 10.

    Kakakin gwamnatin Rasha Dmitry Peskov ya ce babu hannsu a harin, kuma ba sa amfani da irin makaman da aka harba.

    Hotunan da aka wallafa sun nuna gawarwakin mutane da akwatinansu a gefe.

    Karamatorsk da Donetsk na cikin yankunan da mutane ke samu su tsere ta jirgin kasa daga bala'in yaƙin.

  6. Kotu ta yi watsi da tuhuma takwas da gwamnatin Najeriya ke wa Nnamdi Kanu

    Alƙaliyar Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta soke tuhuma takwas daga cikin 15 da gwamnatin Najeriya ke tuhumar madugun 'yan aware na kungiyar IPOB, Nnamdi Kanu.

    Tuhume-tuhumen takwas na cikin laifukan da aka kara kan tuhume-tuhumen da ake yi wa shugaban ‘yan awaren.

    Yayin da take watsi da karar, Mai Shari’a Binta Nyako ta ce zarge-zargen ba su bayyana laifin da wanda ake karar ya aikata ba.

    Mai shari’ar ta ce sato shugaban IPOB din da aka yi da manufar gudanar da bincike abu ne halastacce.

    Ta kuma ce da ma akwai umarnin kamu a kan Kanu bayan tserewa daga kasar a gaban kotu.

    Sai dai lauyoyin da ke kare shi sun dage kan cewa gwamnatin Najeriya ta karya dokar ƙasa da ƙasa tare da take hakkin Kanu, da sato shi daga wata ƙasar a bara.

    Duk da cewa har yanzu hukumomi ba su bayyana inda da kuma yadda aka kama Mista Kanu kuma aka ta so ƙeyarsa ba, dangi da kuma lauyoyinsa na cewa an kama shi ne a ƙasar Kenya cikin wani yanayi mai sarƙaƙiya.

    Gwamnatin Kenya dai ta musanta wannan zargi. An ki ba da belin shugaban kungiyar ta IPOB a zaman na yau.

    Kanu na tsare ne a hannun jami;an ‘yan sanda na farin kaya wadanda suka kawo shi a kotu karkashin tsauraran matakan tsaro.

    Ana zarginsa ne da ayukkan ta’addanci da kuma cin amanar ƙasa kuma yana fuskantar ɗaurin rai-da-rai idan aka same shi da laifi.

  7. Mutanen da aka kashe a harin tashar jirgin ƙasa sun kai 40, in ji Ukraine

    An bayar da rahoton mutuwar mutum 40 bayan wasu rokoki biyu sun faɗa kan tashar jirgin kasa ta Kramatorsk, a cewar gwamnan yankin.

    Da yake magana da BBC, magajin garin Kramatorsk Oleksander Honcharenko ya ce adadin wadanda suka mutun ya karu zuwa 40, ciki har da yara ƙanana 10.

    Sannan kuma mutum 87 sun jikkata a yayin harin, a cewarsa.

    Kyrylenko added that despite the bombardment, evacuations from the region would continue.

    Kyrylenko ya kara da cewa duk da luguden wutar, za a ci gaba da kwashe mutane daga yankin.

  8. Habasha ta dawo da yara 'yan ƙasarta 100 daga Saudiyya

    Ƙasar Habasha wato Ethiopia ta kwashe yara 101 daga Saudiyya a yau Juma'a yayin da take ci gaba da shirinta na komar da dubban 'yan ƙasarta daga Saudiyyar.

    Da yawa daga cikin ‘yan Habashar mazauna Saudiyya 'yan cira-ni ne da ke aiki ba tare da takardun izini ba, wadanda aka tsare cikin wani yanayi maras kyau.

    Sama da mako guda da fara dawo da su, an mayar da ma'aikata kusan 5,000, a cewar wata sanarwa daga ma'aikatar mata da zamantakewa ta Habasha.

    A wani shiri da zai ɗauki tsawon wata 11, hukumomin kasar sun yi alƙawarin dawo da ‘yan kasar Habasha 100,000 gida daga Saudiyya.

    Ana ba wa mutanen mafaka ta wucin gadi da kuma duba lafiyarsu bayan saurkarsu.

  9. Ɓarnar da hari kan tashar jirgin ƙasa ya yi a Ukraine

    Wasu hotuna da BBC ta samu bayan harin roka da Rasha ta kai kan tashar jirgin ƙasa ta Kramatorsk a Ukraine sun nuna irin ɓarnar da harin ya haifar.

    Wani kamfanin sufurin jirgin ƙasan ya ce an kashe aƙalla mutum 30 sakamakon harin na yau Juma'a.

  10. Sojojin Najeriya sun ce sun lalata haramtattun tashoshin tace fetur 30

    Dakarun sojan Najeriya sun lalata haramtattun wuraren tace man fetur 30, sannan suka kwashe sama da lita miliyan 12 na gas da ababen hawa ke amfani da shi (AGO) a ayyukan da suka yi a jihohin Delta, da Rivers, da Bayelsa.

    Daraktan yada labarai na rundunar sojan, Manjo Janar Bernard Onyeuko, shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Abuja.

    "Kamar yadda sanarwar tace, sojojin sun gano tare da lalata haramtattun wuraren tace mai 30, da tankunan ajiye 37, da tanda 31, da manyan jiragen ruwa na katako 12, da na'urorin sanyaya wuri biyu, da ramukan ajiya uku, da ganguna na ƙarfe," a cewarsa.

    “A dunkule, sojojin sun kwato litar mai miliyan 12, da tataccen litar gas 150,000, da lita 4,000 na danyen mai da aka sata, da motocin tanka uku, da motoci uku, da bututu 73, da babura biyu, da motar bas daya, da Toyota kirar Camry daya, da ƙirar Mercedes Benz daya.

    “Bugu da kari, an kama wasu barayin manyan wayoyin wutar lantarki biyu da ke da alaka da lalatawa da kuma sata."

  11. 'Yan sandan Isra'ila sun harbe Bafalasɗine bayan 'ya harbe mutum biyu'

    'Yan sandan Isra'ila sun ce sun harbe wani dan bindiga da ya harbe mutum biyu tare da raunata wasu 12 a wani harbin kan mai-tsautsayi da ya yi a birnin Tel Aviv na Isra'ila.

    Harin dan bindigar ya faru ne a tsakiyar birnin mai cike da wuraren cin abinci da na shan barasa.

    'Yan sanda sun ce an kashe maharin ne sa'oi bayan ya aikata ta'asar a unguwar Jaffa.

    Mai magana da yawun 'yan sandan ta yi karin haske "cewa iyalai da 'yan uwa da abokan arziki na zaune suna 'yan shaye-shaye da tande-tandensu, katsam sai ga wani dan ta'adda ya bude musu wuta".

    Ta ƙara da cewa "nan take ya harbi mutum 10 ya kuma ji wa wasu rauni. A nan ne biyu daga cikinsu suka rasa ransu".

  12. Labarai da dumi-dumi, Ukraine: Harin roka ya kashe mutum fiye da 30 a tashar jirgin ƙasa

    Kamfanin zirga-zirgar jirgin ƙasa a Ukraine ya ce mutum fiye da 30 aka kashe tare da jikkata wasu sama da 100 a harin makamin roka da aka kai kan tashar jirgin ƙasa ta Kramatorsk.

    Kramatorsk na ɗaya daga cikin tashoshin da suka rage da ke aiki a ƙasar, kuma gwamnan yankin Donetsk ya ce akwai dubban mutane a tashar yayin harin da ke yunƙurin hawa jirgi don tserewa daga yankin.

    Shugaban hukumar sufurin jirgin ƙasa na Ukaraine ya ce makaman roka biyu ne suka sauka a tashar.

    Tashar Kramatorsk ta shahara a matsayin ɗaya daga cikin mafiya girman wuraren ɓuya a gabashin Ukraine.

  13. Buhari ya nemi majalisa ta amince da naira tiriliyan huɗu a matsayin kuɗin tallafin mai

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya nemi majalisar tarayyar ƙasar ta ƙara yawan kuɗin tallafin man fetur na kasafin kuɗin 2022 daga biliyan 442 zuwa tiriliyan huɗu.

    Buhari ya buƙaci hakan ne cikin wata wasiƙa da ya rubuta wa 'yan majalisar, inda yake neman su yi wa dokar kasafin kuɗin gyara.

    Cikin wasiƙar wadda Kakakin Majalisar Wakilai Femi Gbajamila ya karanta a zaman majalisa na ranar Alhamis, Buhari ya ambaci hauhawar farashin ɗanyen man fetur sakamakon yaƙi tsakanin Rasha da Ukraine.

    "Kamar yadda kuka sani, an samu sauyi a tattalin arziƙin duniya da kuma na cikin gida wanda ya tilasta neman gyara kan Tafarkin Harkokin Kuɗi na 2022 wanda aka gina kasafin kuɗi na 2022 a kansa," a cewar Buhari.

    A cewarsa, sauyin da za a samu a tafarkin ya haɗa da ƙari a kan hasashen farashin ɗanyen mai daga dala 62 zuwa 73 a kan kowace ganga da aka saka a kasafin kuɗin na 2022.

  14. Mun tafka asara mai yawa a Ukraine - Rasha

    Rasha ta yarda cewa ta "mummunan asara kuma mai yawa" a yaƙin da ta ƙaddamar a Ukaraine, yayin da mamayar ke shiga kwana na 44.

    Mai magana da yawun fadar shugaban ƙasa ta Kremlin, Dmitry Peskov, ya faɗa kafar talabijin ta Sky News cewa asarar da suka yi "babban bala'i ne gare mu".

    Ya ce yana fatan "nan da 'yan kwanaki Rasha za ta cimma muradinta".

    Yanzu dai Rasha ta janye dakarunta daga yankin birnin Kyiv sannan ta mayar da yaƙi kan gabashin Ukraine - amma babu alamun tsagaita yaƙin.

    A ranar 25 ga watan Maris Ma'aikatar Tsaro ta Rasha ta ce an kashe sojojinta 1,351 a yaƙin, amma Ukraine na cewa sun kai 19,000. Sai dai ba za a iya tabbatar da haƙiƙanin adadin ba saboda Rasha ka iya ragewa, Ukraine kuma ka iya ƙarawa.

    Kalaman Mista Peskov na zuwa ne kwana ɗaya bayan korar Rashar daga Majalisar Kare Haƙƙi ta Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD).

  15. Sojojin Rasha sun tsare 'yan Ukraine 130 tsawon wata ɗaya a ƙarƙashin ƙasa

    BBC ta gano shaidar da ke nuna cewa sojojin Rasha sun kama tare da tsare 'yan Ukraine fiye da 100 a wani dakin da ke karkashin kasa na wata makaranta da ke arewacin birnin Chernihiv.

    Sojojin sun rike mutanen ne fiye da wata guda kuma yanayin da suke ciki babu dadi, har ta kai wasu daga cikinsu na barci a tsaye.

    Wani mutum mai shekara 60 na daga cikinsu ga abin da ya ce: "Akwai tazarar rabin mita tsakanina da wani, a tsaye nake barci. Nakan ɗaure kai na da wani tsumma a jikin karfe saboda kar na fadi yayin da nake barci.

    "Na shafe kwana 12 a haka. Dalilin da ya sa na yi wannan juriya shi ne saboda na rayu don 'ya'yana mata da jikokina. Banɗaki a wajen shi ne bokiti, a ciki muke komai."

    Mutum 12 daga cikinsu kuma sun mutu, inda aka bar gawarwakinsu a wajen makarantar.

  16. Maraba

    Barka da shigowa shafin labarai kai-trsaye na BBC Hausa a wannan hantsi na Juma'a tare da ni Umar Mikail.

    Za mu kawo rahotanni na abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman a Najeriya da Nijar, da kuma halin da ake ciki a yaƙin Ukraine.

    Barkanmu da Juma'atu babbar rana.