Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

'Yan sadan Zamfara sun daƙile harin 'yan fashin daji

Wannan shafi ne da ke kawo muku abarai da rahotanni na wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sasssan duniya a ranar da muka shiga sabuwar shekarar 2021.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Imam Saleh

  1. Rufewa

      • Marubuci, Imam Saleh
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multimedia Journalist

    Masu bibiyarmu ta wannan shafi a nan muka kawo ƙarshen kawo muku labarai kai tsaye a wannan rana, da fatan za ku kasance tare da mu gobe idan Allah ya kaimu don ci gaba.

    Imam Saleh ke cewa mu kwana lafiya.

  2. Majalisar wakilan Najeriya za ta soma gyaran kundin tsarin mulki

    Majalisar wakilai za ta ba da kulawa ta musamman ga kokarin gyara kundin tsarin mulkin 1999 da aka yi wa kwaskwarima bayan dawowa daga hutun Kirsimeti da sabuwar shekara, kamar yadda jaridar The Nation rawaito.

    Har ila yau, majalisar na tunanin haɗa hannu da ɓangaren zartarwa gami da duk masu ruwa da tsaki a shirin sake duba kundin tsarin mulkin don tabbatar da kawo sauyi na gari.

    Jaridar ta ce ta samu labarin cewa majalisar ta damu matuƙa cewa gyaran da ake yiwa kundin tsarin mulki a baya ya gaza cimma nasarar da ake nema saboda haka ta kuduri aniyar tabbatar da cewa tsarin da za a yi yanzu bai zama irin waɗanda aka yi abaya ba.

    Shugaban majalisar Femi Gbajabiamila ya ce za a hanzarta yin waɗannan sauye-sauye da zarar majalisa ta koma bakin aiki.

  3. Al Shabab ta ce ita ce ta kai harin ƙunar bakin wake a wajen Mogadishu

    Ƙungiyar masu iƙirarin jihadi ta Al Shabab ta ce ita ce ta kai harin ƙunar bakin wake a wajen Mogadishu babban birnin Somalia wanda ya kashe akalla mutane uku.

    Fashewar ta auku ne a wani ginin da Turkawa ke yi a kan hanyar babban birnin kasar da kuma Afgooye.

    Wata sanarwa daga ma'aikatar harkokin wajen Turkiyya ta yi Allah wadai da harin wanda ta ce ya kashe wani ɗan kasarta da kuma wasu ƴan ƙasar Somaliya biyu.

    Ƙungiyar ta taɓa kai irin wannan hari da ya hallaka mutane 70 a dai wannan hanya da ake aikin samarwa.

    Sojojin Amurka waɗanda ke aiki tare da sojojin ƙasar wajen yaƙar ƙungiyar masu iƙirarin jihadin a halin yanzu tana janye dukkan dakarunta daga Somalia.

  4. Mutumin da ake zargi da kisan mutum 160 a yayin harin Bom a Mumbai ya shiga hannu

    Pakistan ta kama mutumin da ake zargi da jagorantar ƙungiyar masu kishin Islama da aka zargi da kai hare-hare a Mumbai a shekarar 2008.

    An tsare Zaki ur Rehman Lakhvi ne bisa zargin bayar da kudade don taimakawa ta'addanci. Indiya da Amurka sun ce haramtacciyar ƙungiyarsa, mai suna Lashkar- e-Taiba, ita ce ta shirya harin na Mumbai, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum dari da sittin da shida.

    A watan Nuwamban da ya gabata, wata kotu a Pakistan ta yanke wa wanda ya kafa kungiyar, Hafiz Saeed, hukuncin shekaru goma a kurkuku, shi ma bisa zargin taimakawa ta'addanci.

    Pakistan na fuskantar matsin lamba daga wata ƙungiyar sa ido a duniya don yin abin da ya dace da zummar magance ayyukan 'yan bindiga.

    Kwamitin sanya takunkumi na Majalisar Dinkin Duniya ya zarge shi da hannu a hare-hare a ƙasashe kamar Afghanistan, da Iraki da Chechnya.

  5. ''Ba a China kaɗai korona ta samo asali ba''

    Ministan Harkokin Wajen China, Wang Yi, ya yi ikirarin cewa ba wai a ƙsar kaɗai cutar korona ta samo asali ba.

    Ya ce binciken da masana a ƙsar suka gudanar ya tabbatar da cewa ƙwayar cutar ta yaɗu daga sassa daban daban na duniya.

    Mutane da dama a China dai na da irin wannan ra'ayi.

    Ƙasashe da dama na duniya dai na sukar China game da yadda ta yi wasarere da annobar lokacin da ta faro.

    Babu wanda ya san yadda cutar ta farp, amma mutum na farko da ya kamu da ita an same shi ne a birnin Wuhan dake Chinan.

  6. Wata mota ta hallaka mutane hudu a Syria

    Wata mota da ta maƙale a cunkoson ababen hawa ta fashe a arewa maso gabashin Syria.

    Wani yaro da jariri na cikin mutane huɗun da suka mutu yayin aukuwar lamarin.

    Fashewar ta auku ne kusa da kasuwar sayar da kayan lambu ta garin Ras Al -Ayn da ke kan iyakar Turkiyya.

    A wani lamarin kuma, fashewar bam a wata mota a kasuwa a Hasaka, mai nisan kilomita tamanin daga Ras Al -Ayn ta raunata mutane ashirin.

    Kafofin watsa labaran ƙasar sun ce an cafke wani mutum dangane da harin na Hasaka.

  7. 'Yan sadan Zamfara sun daƙile harin 'yan fashin daji

    'Yan sandan Jihar Zamfara sun katse hanzarin wasu 'yan fashin daji a Ƙaramar hukumar Shinkafi tare da ceto mutum ɗaya da aka yi garkuwa da shi.

    Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar 'yan sandan jihar ya fitar a madadin Kwamishina Mohammed Shehu, ya ce lamarin ya faru ne da ƙarfe 4:30 na daren Juma'a.

    SP Shehu ya ce sun samu kiran gaggawa daga mazauna yankin cewa wasu 'yan fashi sun shiga da yawansu da zummar yin garkuwa da mtane.

    Sai dai haɗin gwiwar dakarun rundunar Operation Puff Adder da kuma tubabbun 'yan fashin dajin sun daƙile yunƙurin nasu, a cewar sanarwar.

    Kazalika, 'yan sandan sun ceto wani mai suna Samaila Langa mai shekara 30 da 'yan fashin suka yi garkuwa da shi yayin fafatawar.

  8. Isra'ila ta fi kowace ƙasa saurin yi wa mutane riga-kafin korona

    Isra'ila ta yi wa mutum fiye da miliyan ɗaya allurar riga-kafin cutar korona, wanda shi ne adadi mafi sauri a duniya.

    Ƙasar na da ma'aunin 11.55 na saurin yi wa kowane mutum 100 allurar, sai Bahrain mai 3.49 da kuma Birtaniya mai 1.47, a cewar alƙaluman shafin da ke bin sawun riga-kafin na Jami'ar Oxford.

    Tun a ranar 19 ga watan Disamba Isra'ila ta fara yi wa mutanenta riga-kafin, inda ake yi wa kusan mutum 150,000 a kowace rana tare da bai wa tsofaffi da ma'aikatan lafiya fifiko.

    Faransa ta yi wa mutum 138 riga-kafin jumilla ya zuwa 30 ga watan Disamba.

    Sama da mutum miliyan 1.8 ne suka mutu a faɗin duniya sakamakon cutar korona, wadda ta ɓulla a watan Disamban 2020.

    Cibiyar Our World in Data da kuma wata gidauniyar ilimi ne suke tattara bayanan gudanar da riga-kafin a faɗin duniya.

    Sukan duba yawan mutunen da aka yi wa allurar a karon farko. Akasarin riga-kafin da aka amince da su sau biyu ake yi, waɗanda ake yinsu da tazarar fiye da mako ɗaya a tsakani.

  9. El-Rufai ya yi wa 'yan gidan yari 12 afuwa

    Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai ya bayar da umarnin sakin mutum 12 daga gidan yari.

    Wata sanarwa da mai ba shi shawara kan kafafen yaɗa labarai ya fitar ta ce mutanen sun ƙunshi 10 da aka yanke wa hukuncin zaman shekara uku ko fiye, inda ya rage musu saura wata shida ko ƙasa da haka.

    Muyiwa Adekeye ya ce an saki sauran mutum biyun ne sakamakon yawan shekarunsu.

    "An ɗaure Gabriel Olugbenga tsawon shekara bakwai bisa laifin kisa a shekarar 2016. Shekararsa 60 kuma saura wata shida ya kammala zaman gidan yarin, wanda ya kamata ya gama a Yunin 2021," in ji shi.

    "An ɗaure Tunde Ikuenaya shekara huɗu a watan Nuwamba na 2017. Shekararsa 64 kuma ana sa ran sai Maris 2021 zai kammala zaman gidan yarin."

    Kazalika, El-Rufai ya rage adadin hukuncin da aka yanke wa wasu mutum uku zuwa shekara biyar "saboda sun yi zaman shekara 10 ko fiye kuma sun nuna ɗa'a".

    ‘’Ifeanyi Chiebuike Nweke da Mohammed Mamman Santare da Samaila Danjuma, an yanke musu hukunci ne a lokuta daban-daban sakamakon laifin kisa."

    Nasir El-Rufai ya yi musu afuwar ne a matsayinsa na gwamnan Jihar Kaduna, kamar yadda sashe na 212 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya ya ba shi dama.

  10. Yadda aka bankwana da shekarar 2020

  11. Yadda talla ke katse wa yara mata burinsu a Kano

    Rashin samun ilimi ga yara mata a Arewacin Najeriya na daga cikin matsalolin da ke janyo wa matan koma-baya a bangarori daban-daban na rayuwa.

    Kiyasin masu bincike ya nuna cewa jihohin yankin irin su Sokoto da Bauchi na da sama da kashi 80 cikin 100 na yara mata wadanda ba sa samun damar kammala karatunsu na sakandare.

    Sau da dama wasu gwamnatoci sun sha yunkurin yin dokokin da za su tilasta wa iyaye sanya yaransu a makaranta, sai dai matakin na gamuwa da cikas saboda matsaloli kamar talauci da rashin kyakkyawan yanayin karatu, yaran kuma na fadawa cikin manyan matsalolin rayuwa sanadiyyar haka.

    A filinmu na Gane Mani Hanya, Haruna Ibrahim Kakangi ya duba mana lamarin a wasu kauyukan jihar Kano.

  12. Labarai da dumi-dumi, Sai an je zagaye na biyu a zaɓen Nijar

    Hukumar zaɓen Nijar CENI ta tabbatar da cewa za a je zagaye na biyu a zaɓen shugaban ƙasar Jamhuriyar Nijar.

    An cimma matakin ne saboda babu jam'iyyar da ta ci kashi 50 ko fiye a zaɓen.

    Kamar yadda jadawalin hukumar zaɓe ya nuna, ranar 21 ga watan Fabarairun 2021 ne za a gudanar da zagaye na biyun.

    Sakamakon zaɓen da CENI ta bayyana yanzu ya nuna cewa ɗan takarar jam'iyya mai mulki ta PNDS Tarraya, Bazoum Mohamed, shi ne ya lashe kashi 39,33 cikin 100, inda yake da kuri'a 1, 879, 000.

    Sai kuma Mahamane Ousmane na jam'iyyar RDR Canji da ya lashe kashi 16.99 cikin 100 kuma ya samu ƙuri'a 811,838.

    Hakan na nufin za a fafata zaɓen zagaye na biyu tsakanin 'yan takarar guda biyu, waɗanda su ne kan gaba a zagayen farko.

  13. An fara bayyana sakamakon zaɓen shugaban ƙasar Nijar

    An fara bayyana sakamakon zaɓen shugaban ƙasar Nijar da aka gudanar ranar 27 ga watan Disamba.

    Shugaban hukumar zaɓen, Barista Isiaku Sunna ne yake karanto sakamakon a Palais des congrès, wanda zai ƙunshi har da na 'yan majalisar dokoki.

    Ya ce hukumar zabe ba ta gayyaci mutane da yawa ba saboda matakan kariya daga cutar korona.

    Sakamakon farko-farko na zaɓen ya nuna cewa ɗan takarar jam'iyya mai mulki ta PNDS Tarayya Bazoum Mohammed ne yake kan gaba.

    Sai kuma Alhaji Mahamane Ousmane na jam'iyyar RDR Canji da yake biye masa baya.

  14. Dubban mutane na halartar casu a Faransa duk da cutar korona

    Mutum fiye da 2,500 ne suka taru domin yin wani haramtaccen casu a Faransa yayin da ƙasar ke fama da annobar cutar korona.

    Bikin wanda aka gudanar a wani wurin ajiyar kaya da ke Brittany, an fara shi ne tun ranar Alhamis kuma har ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto ba su gama cashewa ba.

    Da yawa daga cikin masu raƙashewar sun fito ne daga ƙasashen Birtaniya da Spain, a cewar 'yan sanda.

    Masu sharholiyar sun yi arangama da 'yan sanda har ma suka ƙona wata mota tare da jifan 'yan sandan da suka yi yunƙurin hana shagalin. An jikkata aƙalla 'yan sanda uku.

    Wata sanarwa da hukumomin yankin suka fitar ta ce 'yan sanda "sun yi ƙoƙarin hana taron amma suka fuskanci tirjiya daga 'yan sharholiyar".

    Wani da ya je wurin mai suna Jo, ya faɗa wa AFP cewa "mutane 'yan ƙalilan ne suka mutunta dokokin bayar da tazara" a wurin casun.

    Wasu daga cikinsu sun kwana a motocinsu kafin daga baya su koma su raƙashe, a cewar rahoton Le Monde.

    Har wa yau, wasu daga cikinsu sun ce sai sun kai har Lahadi, yayin da wasu ke cewa ma har sai Talata.

  15. Brazil ta janye wa talakawa tallafin cutar korona na wata-wata

    Miliyoyin mutane a Brazil na fuskantar rashin tabbas kan kudin kashewa bayan da gwamnati ta ki sabunta wani shirin tallafi da aka kirkira domin rage radadin annobar korona.

    Tuni cutar ta kashe mutum kusan 200,000 a kasar.

    Wa'adin shirin tallafin ga talakawa wanda ya kai dala130 a duk wata, ya kare a jajiberin sabuwar shekara.

    Shugaba Jair Bolsonaro wanda ya sha yin watsi da girman annobar cutar, ya ce ana bin ƙasarsa bashi sosai kuma ba za ta iya ci gaba da bayar da kudaden tallafin ga jama'a har abada ba.

    Wakilin BBC ya ce: ''An samu karuwar masu cutar korona da wadanda take kashewa cikin wata guda ya gabata kuma ba a sa ran za a soma yi wa jama'a allurar riga-kafi sai akalla tsakiyar watan Faburairu''.

    Masana tattalin arziki na cewa kawo karshen tallafin kudin zai jefa mutum fiye da miliyan 20 cikin matsanancin talauci.

  16. EFCC ta kama mutum 21 da zargin zamba ta intanet

    Jami'an hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa a Najeriya reshen Jihar Legas sun kama mutum 21 bisa zargin aikata zamba ta intanet.

    EFCC ta ce ta kama mutanen ne na wata ƙungiyar aikata laifuka ta intanet yayin wani samame da asubahin ranar Laraba bayan ta samu wasu bayanan sirri game da ayyukan nasu.

    Bayan kama sun ne kuma, hukumar ta ƙwace ababen hawa guda 12 da suke amfani da su da kwamfutar laptop da kuma wayoyin hannu.

    Hukumar ta bayyana sunayen mutanen kamar haka: Shittu Yakubu, Akinsola Afeez, Adeniyi Joseph, Opeyemi Wahab, Idris Sunday, Lawal Moshood, Jubril Yusuf, Olusegun Mohammed, Adekunle Adesanya, and Damilola Abijide.

    Sauran su ne Sola Adio, Oladipo Ademola, Damilola Adewale, Akinsola Ridwan, Ogunlaye Damilare, Falaye Peters, Magnus Toni, Onanuga Ahmed, Bolarinwa Segun, Onanuga Olawale, and Ayomide Afeez.

    EFCC ta ce za ta gurfanar da su a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

  17. Sojojin Isra'ila sun raunata matashin Falasɗinawa

    Wani Bafasdine na cikin mawuyacin hali bayan da sojin Isra'ila suka harbe shi a jiya Juma'a lokacin wani artabu a wani kauye da ke kudu da Hebron a Gabar Yamma ta Yahudawa suka mamaye.

    Jami'an Falasdinu sun ce jikin matashin mai shekara 24, ya shanye tun daga wuya har zuwa kafafu.

    Rundunar sojin Isra'ila ta ce an harbe shi ne a lokacin abin da ta kira 'tarzoma' bayan sojoji sun yi kokarin kwace wani haramtaccen kayan aikin gini daga wurinsa.

  18. Ƙarin mutum 1,074 sun kamu da cutar korona a Najeriya

    Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum biyar da suka mutu sakamakon cutar korona sannan 1,074 sun kamu da cutar a ranar Juma'a.

    Sabbin alƙaluman da hukumar ta wallafa a shafinta na twitter sun nuna cewa jihar Legas ce ke kan gaba da mutum 642.

    Jihar Kaduna ta zama ta biyu da yawan mutum 92, sai kuma jihar Rivers mai mutum 78 sannan birnin tarayyar Abuja na da mutum 66 da suka kamu da cutar.

    A wannan karon jihar Gombe ta yi sama da mutum 66 inda kuma jihar Kano mai mutum 35 ke biye da ita.

    Jihar Ogun na da masu cutar 31, Katsina 22, Plateau 20, Abia 7, sai kuma jihohin Niger da Oyo masu mutum 4 kowacce.

    Akwa Ibom na da 3 sannan Delta na da 2.

    Da wannan adadi, jumillar mutum 88,587 suka harbu da cutar a Najeriya, yayin da 1,294 suka mutu sannan aka sallami 74,373 bayan sun warke.

  19. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da haɗuwa a wannan hantsi na Asabar tare da fatan za ku biyo ni Umar Mikail domin samun labaran abubuwan da ke faruwa musamman a Najeriya da Nijar.

    Kazalika, za mu bi lungu da saƙo na sassan duniya.