Ƙarin mutum 10 ne suka mutu sakamakon cutar korona a Najeriya ranar Litinin, a cewar alƙaluman hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa.
Sabbin alƙaluman da ta wallafa a shafinta na intanet ya kuma nuna cewa ƙarin mutum 397 ne suka kamu da cutar.
Ta ce an samu sabbin kamuwar ne a jiha 18 har da Abuja kuma sun haɗa da Legas (144) da Filato (83) da Kaduna (48) da Adamawa (36) da Rivers (22) da Oyo (16) da Kebbi (10).
Sauran jihohin su ne: Nasarawa (7), Sokoto (7), Abuja (5), Kano (5), Edo (4), Jigawa (3), Ogun (2), Akwa Ibom (2), Neja (1), Bauchi (1), Zamfara (1).
Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 84,811 ne suka kamu da cutar a Najeriya, 1,264 da cikinsu sun mutu sannan 71,357 sun warke.