Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Mutum 12 sun mutu kan hanyar Kaduna zuwa Abuja

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye, sai kuma gobe Alhamis idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin a yau.

    • Tunisia za ta ƙara tsawaita wa'adin dokar hana fita
    • Najeriya ta sanar da ranakun hutun Kirisimeti da sabuwar shekara
    • MDD ta yi tur da matakin Trump na yafe wa sojojin hayar Amurka da suka yi kisa a Iraƙi
    • Mahara sun kashe 'mutum 90' a Ethiopia
    • Dakarun MDD sun ƙwato garin Bambari a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai.

  2. LABARAN WASANNI NA YAMMA - 23/12/2020

  3. Mutum 12 sun mutu kan hanyar Kaduna zuwa Abuja

    Mutum 12 sun mutu, 25 sun samu raunuka sakamakon wani haɗarin mota da ya faru kan hanyar Kaduna zuwa Abuja a ranar Laraba.

    Kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Samuel Aruwan ya tabbatar wa BBC da faruwar lamarin.

    Kwamishinan ya ce cikin abubuwan da suka jawo haɗarin har da rashin kyawun hanya da tuƙin ganganci da kuma gudu da mota.

    Ko a farkon watan Disamba sai da mutum 16 suka mutu sakamakon haɗarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zaria.

  4. Mahara sun kashe 'mutum 90' a Ethiopia

    Wasu mahara da ba a san ko su wane ne ba sun kashe aƙalla mutum 90 a wani ƙauyen jihar Benishangul-Gumuz da ke Ethiopia da safiyar Laraba, kamar yadda mazauna yankin suka shaida wa BBC.

    Harin na zuwa ne kwana guda bayan Firaiministan ƙasar, Abiy Ahmed tare da manyan jami'an gwamnatin ƙasar da jami'an soji sun kai ziyara yankin domin tattauna batun yawan rikice-rikicen ƙabilancin da ake samu.

    Wata malamar jinya a wani asibitin yankin da lamarin ya faru ta shaida wa BBC cewa akwai sama da mutum 30 da suka samu raunuka an kwantar da su a asibiti.

    Wasu sun samu raunuka ne sakamakon harbin bindiga wasu kuma sun samu raunin ne sakamakon harin wuƙa.

    Mai magana da yawun gwamnatin jihar, Beyene Melese, ya ɗora alhakin harin kan waɗanda ya kira "masu adawa da zaman lafiya".

    "Babu tabbacin mutanen da aka kashe, sai dai muna da labarin cewa adadinsu na da yawa," kamar yadda ya shaida wa BBC.

  5. MDD ta yi tur da matakin Trump na yafe wa sojojin hayar Amurka da suka yi kisa a Iraƙi

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi Allah-wadai da yafiyar da Shugaban Amurka Donlad Trump, ya yi wa sojojin hayar Amurka da suka kashe fararen hula a Iraƙi.

    Hukumar kare haƙƙin bil'adama ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce sanarwar yafiyar da aka yi a ranar Talata, za ta iya tunzura wasu su aikata makamancin laifin.

    Waɗanda aka yafe ma wa, wasu dakaru huɗu ne na wani kamfanin tsaro mai zaman kansa na Amurka mai suna Blackwater security firm wanda ke samar da sojojin haya.

    An kama su da laifin hannu a kashe wasu fararen hula 14 a wani shataletale mai cike da cunkoso a Bagadaza a 2007.

    Dakarun sun buɗe wuta ne yayin da suke raka wasu ayarin motoci na jami'an diflomasiyya na Amurka a wurin.

  6. Kun san abin da Buhari ya ce game da bodar Najeriya da Nijar?

  7. Hazard zai buga wa Real Madrid wasa da Granada

    Real Madrid ta bayyana 'yan wasa 24 da za su fuskanci Granada a wasan cin kofin La Liga ranar Laraba, cikinsu har da Eden Hazard.

    Rabon da dan kwallon tawagar Belgium ya buga wa Real tamaula tun raunin da ya yi a karawa da Alaves ranar 28 ga watan Nuwamba.

    Hazard na fama da yawan yin raunin tun bayan da ya koma Real Madrid da taka leda daga Chelsea.

    Sauran 'yan wasan da za su fafata da Granada har da Isco da kuma Vinicius Junior.

    Sai dai Real za ta buga karawar ta ranar Laraba ba tare da Luca Modric ba, wanda ya yi rauni a wasan da Madrid ta yi nasara a kan Eibar da ci 3-1 ranar Lahadi

  8. Najeriya ta sanar da ranakun hutun Kirisimeti da sabuwar shekara

    Gwamnatin Najeriya ta sanar da ranakun hutun Kirisimeti da sabuwar shekara.

    A wata sanarwa da ma'aikatar harkokin cikin gida ta fitar, ranakun Juma'a 25 ga watan Disamba da Litinin 28 ga watan Disamban 2020 da kuma 1 ga watan Janairun 2021 za su kasance ranakun hutun Kirisimeti da ranar rabon kyaututtuka (Boxing Day) da kuma sabuwar shekara.

    Ministan harkokin cikin gida na Najeriya, Rauf Aregbesola ya ja hankalin Kiristoci da su yi koyi da halaye na gari na Yesu Almasihu.

  9. Tunisia za ta ƙara tsawaita wa'adin dokar hana fita

    Ƙasar Tunisia za ta kara tsawaita dokar hana fita ta dare har zuwa tsakiyar Janairun shekara mai zuwa, kamar yadda hukumomin lafiya suka bayyana.

    An sanar da wannan matakin ne a ranar daren Talata, bayan shawarwarin da kwamitin da ke yaƙi da annobar korona ya bayar.

    Sama da mutum 120,000 aka tabbatar da sun kamu da cutar tun a watan Maris, sai dai akasarin waɗanda suka kamu da cutar a 'yan watannin baya suka kamu.

    Ƙasar ta ce ba a samu sabon nau'in cutar ba a ƙasar, amma ana sa ran za a samu riga-kafin cutar zuwa Afrilu mai zuwa.

    Alƙaluma sun nuna cewa ana samun kusan mutum 40 a rana da ke mutuwa sakamakon cutar, haka zalika, yanzu haka akwai marasa lafiya a bisa kashi 77 cikin 100 na gadajen gaggawa da ake kwantar da marasa lafiya a faɗin ƙasar.

  10. 'Yan bindiga sun kashe mai fafutikar kyautata zaɓe a Afghanistan

    'Yan bindiga a Afghanistan sun kashe shugaban kungiyar sa ido kan zabe mafi girma a kasar.

    Maharan sun bude wuta kan Muhammad Yusuf Rashid ne yayin da ake tuka shi zuwa wurin aiki a Kabul, babban birnin kasar.

    Yusuf Rashid ne ke jagorantar wata kungiya mai fafutukar ganin ana zaben gaskiya da adalci a Afghanistan.

    Shi da direbansa, an dauke su zuwa asibiti, kuma daga dukkansu sun rasu.

    Yusuf Rashid dai ya yi suna a Afghanistan wajen bayyana damuwa kan yadda ake razana masu zabe da kuma tafka magudi.

    Ya zuwa yanzu babu wanda ya dauki alhakin kai harin.

    Kisan nasa shi ne na baya-bayan nan cikin jerin kashe-kashe na gilla da ake aikatawa a Afghanistan.

  11. Dakarun MDD sun ƙwato garin Bambari a Jamhuriyar Tsakiyar Afirka

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce ta ƙwace garin Bambari na Jamhuriyar Tsakiyar Afirka daga hannun 'yan tawayen da suka karɓe shi jiya Talata.

    Wani mai magana da yawun majalisar ya ce dakarunta na kiyaye zaman lafiya ne da kuma sojin kasar ke iko da garin a yanzu bayan da suka kora 'yan bindigar cikin daji.

    Ya ƙara da cewa cewa fararen hula da suka tsere daga garin sakamakon faɗan sun fara komawa.

    Ranar Lahadi mai zuwa ake sa ran gudanar da zaɓe a ƙasar.

    Wakiliayr BBC ta ce gwamnati na zargin tsohon Shugababn Ƙasar, Francois Bozize da haɗa karfi da 'yan tawayen domin yin juyin mulki - zargin da shi kuma ya musanta.

    Rasha da Rwanda sun tura ƙarin ɗaruruwan sojoji domin ƙarfafa gwamnatin ƙasar.

  12. Jihar Kwara ta saka dokar kulle ta dare

    Gwamnatin Jihar Kwara ta saka dokar kulle daga ƙarfe 12:00 na dare zuwa 4:00 na yamma da zummar daƙile yaɗuwar annobar cutar korona.

    Umarnin kafa dokar na cikin sabbin matakan kariya daga cutar wanda kwamitin yaƙi da korona na jihar ya fitar a yau Laraba.

    Da yake zantawa da manema labarai a birnin Ilorin na jihar, Kwamishinan Lafiya kuma Shugaban Kwamitin Dakta Raji Rasaq ya ce dokar za ta fara aiki ne daga gobe Alhamis, 24 ga Disamba.

    Sauran matakan sun haɗa da dakatar da ma'aikatan gwamnati zuwa ofis, inda ma'aikatan da ya zama dole ne kaɗai za su riƙa zuwa aiki.

    Kazalika, kwamishinan ya ce makarantu za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai an ji daga garesu.

    "Wajbii ne wuraren ibada kar su ɗauki mutane fiye da kashi 50 cikin 100 na abin da suka saba ɗauka domin bayar da tazara."

    Jihar Kwara ta samu jumillar mutum 1,328 da suka kamu da cutar korona ya zuwa daren Talata, a cewar NCDC. 31 daga cinisu sun rasu, yayin da 1,094 suka warke.

  13. Babu laifi Musulmai su yi amfani da riga-kafin korona - Malaman Dubai

    Majalisar Fatawa ta Daular Larabawa wato UAE ta ce babu laifi ga Musulmai idan suka yi riga-kafin cutar korona ko da kuwa tana ɗauke da abin da addini ya haramta kamar sassan alade.

    Kamfanin dillancin labaran ƙasar na WAM ya ruwaito jiya Talata cewa malaman sun ce za a iya wa Musulmi allurar cutar ko da kuwa akwai abin haram matuƙar babu wani zaɓi.

    Wannan fatawa tasu na zuwa ne yayin da wasu al'ummar Musulmi ke nuna shakku game da kayan haɗin allurar, wadda ake tunanin tana ƙunshe da ababen da Musulunci ya haramta ci ko shan su.

    "Riga-kafin korona na cikin abubuwan da aka saka su a matsayin kayan kariya ga ɗan Adam kamar yadda Musulunci ya tanada, musamman a lokutan annoba, inda mai lafiya ke shiga haɗarin kamuwa, wanda zai iya jawo haɗari ga al'umma baki ɗaya," a cewar majalisar.

    A jiya Talata ne Dubai ta sanar cewa za ta fara yi wa 'yan ƙasar riga-kafin korona a yau Laraba.

  14. Jam'iyyar Hama Amadou ta mara wa Mahaman Ousman baya a zaɓen Nijar

    Jami’yar Moden Lumana ta jagoran hamayyar Jamhuriyar Nijar, Hama Amadou, ta umurci magoya bayanta su kaɗa wa tsohon shugaban ƙasa Mahaman Ousman na jam'iyyar RDR Canji kuri’a a zaɓen shugaban ƙasa.

    A ranr Lahadi mai zuwa ne 'yan Nijar za su nufi rumfunan kaɗa ƙuri'a domin zaɓar shugaban ƙasa da 'yan majalisa.

    Yayin wani taron manema labarai da suka kira a jiya Talata a ofishin Moden Lumana da ke birnin Yamai, shugabanin kwamitin ƙolin jam'iyyar sun ce sun ɗauki matakin ne "saboda ci gaban Nijar".

    “Mun faɗa wa duk wani mai kishin ƙasa da ke so ya ga Nijar ta kasace cikin kwanciyar hankali da zama lafiya ya miƙa kuri’arsa ga tsohon shugaban a matsayin ɗan takarar da Lumana ta amince da shi," in ji Sani Malan Mahaman, sakataren jam'iyyar.

  15. Buhari na jagorantar zaman Majalisar Zartarwa

    Shugaba Muhammadu Buhari na Najeiya na jagorantar zaman Majalisar Zartarwa ta bidiyo na 29 a Fadar Aso Rock Villa da ke Abuja.

    Buhari bai jagoranci taron makon jiya ba sakamakon yana hutun aiki na mako ɗaya a Daura, mahaifarsa da ke Jihar Katsina. Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo ne ya jagoranci zaman.

    Ana sa ran majalisar wadda ta ƙunshi dukkanin ministoci da manyan jami'an gwamnati, za ta amince da aiwatar da wasu ayyuka a faɗin ƙasa baki ɗaya.

    Majalisar kan yi irin wannan zama duk ranar Laraba domin tattauna ayyukan gwamnati, kamar yadda takwarorinsu na jihohi ke yi.

    A safiyar yau Laraba ne ƙungiyar ASUU ta malaman jami'o'i a Najeriya ta janye yajin aikin da ta shafe wata tara tana yi sakamakon wasu buƙatu da ta ce gwamnati ta gaza biya mata.

  16. Mutum miliyan 4.5 ne suka ziyarci Masallacin Harami bayan sake buɗe shi

    Fiye da mutum miliyan huɗu da rabi ne suka ziyarci Masallacin Harami da ke Makkah da kuma Masallacin Annabi na Madina tun daga watan Oktoban 2020 bayan sake buɗe su.

    Hukumar da ke kula da masallatan ta ce an kula da maziyartan duk da irin yawansu ta hanyar tilasta musu bin dokokin kare kai daga kamuwa da cutar korona.

    A ranar 4 ga watan Oktoba ne gwamnatin Saudiyya ta sanar da sake buɗe masallatan bayan sun shafe watanni a kulle sakamakon yaɗuwar annobar cutar ta korona.

    A karon farko, an ƙyale masu bauta kashi 30 cikin 100 ne kacal domin gudanar da ayyukan Umara, inda mutum 6,000 suka riƙa shiga a kowace rana.

    A karo na biyu kuma, an bar kashi 75 na masu ibada, inda maniyyata aikin Umara 15,000 suke shiga tare da 40,000 na masallata.

    Sai a farkon watan Nuwamba ne kuma aka fara ƙyale 'yan ƙasashen waje gudanar da Umara. Mutum 20,000 ne aka yarje wa su shiga a kowace rana tare da masallata 60,000.

  17. Trump ya yi fatali da tallafin dala biliyan 900 da za a bai wa Amurkawa

    Shugaban Amurka Donald Trump ya yi fatali da wani shirin ba da tallafin korona na dala biliyan 900 da Majalisar Wakilai ta amince da shi ranar Lahadi bayan kwashe watanni ana ce-ce-ku-ce kansa.

    A cikin wani bidiyo da ya saka a shafinsa na Twitter, Mista Trump ya kushe bayanan da kudurin dokar ya ƙunsa.

    "Ƙudirin dokar da suke son aikowa ofishina ya bambanta da wanda ake tsammani. Wannan abin kunya ne," in ji shi.

    Ya ƙara da cewa: "Misali, kudurin nan mai shafuka fiye da 5,000 wanda babu dan majalisar da ya karance shi saboda yawa da sarkakiyar da yake da ita, an kira shi kudurin dokar tallafin Corona, amma kusan ba shi da alaka da covid-19."

    Daga cikin tanade-tanaden ƙudirin akwai rarrabawa mafi rinjayen al'ummar Amurka dala 600 kyauta kowane mutum ɗaya.

    Ana sa ran Mista Trump wanda zai bar mulki ranar 20 ga watan Janairu, ya saka wa dokar hannu bayan amincewa da ita da majalisar ta yi ranar Litinin da dare.

  18. Labarai da dumi-dumi, ASUU ta janye yajin aiki

    Ƙungiyar ASUU ta malaman jami'o'i a Najeriya ta janye yajin aikin da ta shafe wata tara tana yi.

    Shugaban kungiyar Biodun Ogunyemi ne ya sanar da haakn a safiyar Laraba a Abuja.

    Ya ce matakin ya biyo bayan tattaunawar da majalisar zartarwar kungiyar ta yi.

    A yammacin jiya Talata ne ASUU da gwamnatin tarayyya ƙarƙashin jagorancin Ministan Ƙwadago Chris Ngige suka shiga tattaunawa, wadda ministan ya ce ta kai kashi 98 cikin 100 a kammala.

  19. 'Dan bindiga ya kashe 'yan sanda uku a Faransa

    Wani ɗan bindiga ya kashe 'yan sanda uku bayan an nemi agajinsu zuwa wani gida da aka samu rahoton cin zarafi a Faransa.

    Wata mata ce ta hau saman rufin wani gida a kauyen Saint-Just a yau Laraba jim kaɗan kafin faruwar lamarin.

    Mutumin ya kashe ɗan sanda ɗaya sannan ya raunata ɗaya. Daga baya ya cinna wa gidan wuta kuma ya harbe wasu 'yan sandan biyu bayan sun isa wurin. Sa dai an ceto matar.

    Har yanzu 'yan sanda na neman wanda ake zargin mai shekara 48, wanda aka ce da ma ana shan fama da shi game da neman haƙƙin riƙe 'ya'yansa.

    Magajin Garin Saint-Just, François Chautard, ya faɗa wa kafar yaɗa labarai ta Le Figaro cewa gidan ya ƙone ƙurmus amma 'yan sanda na ƙoƙarin gano ko mutumin yana ciiki.

    A gefe guda kuma, wata majiyar 'yan sanda ta faɗa wa BFMTV cewa mutumin ya tsere.

    Ministan Harkokin Cikin Gidan Faransa Gérald Darmanin ya bayyana sunayen 'yan sandan da aka kashe; Brig Arno Mavel mai shekara 21 da Lt Cyrille Morel ɗan shekara 45 da kuma Adjutant Rémi Dupuis mai shekara 37.

  20. Cutar korona a Najeriya: Mutum huɗu sun rasu, 999 sun kamu ranar Talata

    Hukumar NCDC mai yaki da yaduwar cutuka a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutum 999 da suka kamu da cutar korona ranar Talata.

    Kamar yadda ta wallafa a shafinta na intanet, ƙarin mutum huɗu sun rasu sakamakon cutar.

    Sabbin alƙaluman sun nuna cewa an samu ƙarin ne a Abuja (416) da kuma jihohin Legas (324) da Kaduna (68) da Filato (42) da Kwara (32) da Kano (24),.

    Sauran su ne: Gombe (14), Sokoto (12), Yobe (12), Akwa Ibom (11), Bayelsa (10), Rivers (7), Bauchi (7), Ogun (6), Oyo (5), Edo (4), Taraba (4), Jigawa (1).

    Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 79,789 ne suka harbu da cutar a Najeriya, 68,879 daga cikinsu sun warke tare da mutuwar mutum 1,231 tun daga watan Fabarairun 2020 da cutar ta ɓulla a ƙasar.