Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Janar Buratai ya kai ziyara garin Kankara

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. Rufewa

    Nan za mu dakatar da kawo labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.

    Da fatan za ku kasance da mu zuwa gobe inda za mu shafe yinin Litinin muna kawo labarai da rahotannin da suka shafe ku kai tsaye.

    Za ku iya zuwa har ƙasan wannan shafin domin karanta abubuwan da suka faru a yinin Lahadi.

  2. Karon farko shugaban Algeria ya fito bainar jama’a

    A karon farko Shugaban kasar Algeria Abdulmajid Tebboune ya fito bainar jama'a, tun bayan kwantar da shi da aka yi a wani asibitin kasar Jamus sakamakon kamuwa da annobar korona watanni biyu da suka gabata.

    A wani bayani da ya yi ta Talabijin, Shugaba Tabboune mai shekara 75, ya ce yana samun sauƙi, kuma yana nan tafe zuwa gida ba da dadewa ba.

    Bayan shugaban ƙasar ya tafi jinya Firaminisa Abdelaziz Djerad ke tafiyar da gwanatin Algeria da annobar korona ta ƙara jefa wa cikin matsalar tattalin arziki.

    Shugaba Tebbouneya ce yana yi wa Allah godiya, da kuma jinjina ga asibitin sojoji da likitocin kasar Jamus, kuma yana nan tafe zuwa gida.

  3. Iraƙi ta ce sojojinta sun kashe mayaƙan IS 42

    Rundunar sojin Iraƙi ta ce aƙalla mayaƙan IS 42 dakarunta suka kashe cikin kwana biyu a wani farmaki da suka kaddamar a garin Mosul.

    Kakakin sojin ƙasar ya ce dakarun rundunar da yake da ta’addanci da ke samun taimakon dakarun ƙawance da Amurka ke jagoranta sun gano wani kogo da mayakan IS ke ɓuya.

    Ya ce daga cikin waɗanda aka kashe akwai manyan mayakan IS.

    Mayakan IS sama da 12,000 ake tunanin suna cikin Iraƙi.

  4. Janar Buratai ya kai ziyara garin Kankara

    Babban hafsan sojan ƙasa na Najeriya Janar Tukur Buratai ya isa garin Kankara inda aka sace ɗalibaida dama a makarantar sakandare.

    Gwamnatin Katsina ta ce ɗalibai 333 suka ɓata da ba a gani ba a makarantar.

    Bayanai sun ce Janar Buratai ya gana da rundunar soji da ta kaddamar da binciken gano ɗaliban da aka sace a ranar Juma’a.

    Sannan ya kuma gana da ɗaliban da suka samu hanyar tsira daga daji suka dawo gida.

    Babban Hafsan sojan na Najeriya ya tafi Kankara ne tare da tawagar gwamnatin Tarayya da ta ƙunshi ministan tsaro Janar Salihi Magashi mai ritaya da kuma mai ba shugaban ƙasa shawara kan sha'anin tsaro

    Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya shaidawa BBC cewa yara da dama sun gudo tare da cewa 10 ne kawai suka rage hannun ƴan bindiga.

    Ya kuma ce jami’an tsaro sun yi wa yankin Kankara ƙawanya da suke tunanin ƴan bindigar na garkuwa da yaran da suka sace.

  5. Najeriya da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa sun inganta hulɗa

    Ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da Najeriya sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar inganta hulɗa a tsakaninsu inda suka amince su kafa kwamitin haɗin guiwa ɗon bunƙasa hulɗodinsu na siyasa da tattalin arziki da tsaro da kasuwanci da al’adu da shari’a da kuma saka jari.

    Kamfanin dillacin labarai na Daular Larabawa WMA ya ce an ƙulla yarjejeniyar ne a ma’aikatar harakokin wajen Najeriya a Abuja tsakanin jekadan Daular Larabawa Fahad Obaid al-Taffaq da kuma ministan harakokin wajen Najeriya Affairs Geoffrey Onyeama

    Tun a 1982 ƙasashen biyu suka fara ƙulla alaƙa tsakaninsu amma a 2009 Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa ta bude ofishin jekadanci a Abuja.

  6. An yi wa ƴan bindiga da suka sace ɗalibai ƙawanya a Kankara - Buhari

    Mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya ce jami'an tsaro sun yi wa yankin da suke tunanin ƴan bindiga na garkuwa da ɗaliban makaranta da suka sace a Kankara jihar Katsina arewa maso yammacin ƙasar.

    Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa yaran da suka tsere daga hannun maharan sun ce yara 10 ne ke hannun ɓarayin ƙasa da yawan ɗaliban da malaman makarantar suka bayyana.

    "Wasu daga cikin yaran da suka gudu daga daji sun ce yara 10 ne ƴan bindigar suke garkuwa da su," in ji shi.

    Sai dai ya ce sai an bincika sannan domin sun warwatsu a daji saboda ɗimauta daga ƙarar harbe-harben bindiga.

    Ya kuma ce kusan ɗalibai 200 suka dawo gida kuma wasu daga cikin iyayen yaran sun karɓi ƴaƴansu da suka fito daga daji yayin da kuma ake ƙoƙarin tantance yawansu da waɗanda suka dawo.

  7. Kusan sa'a 48 kenan ba a ji ɗuriyar ɗaliban Kankara da aka sace

    Kusan sa'a 48 kenan babu wani labari game da ɗaliban makarantar sakandaren Kankara ta jihar Katsina da ke arewacin Najeriya da ƴan bindiga suka yi awon gaba da su.

    Iyayen ɗaliban makarantar na jiran tsammani game da labarin ƴaƴansu, yayin da fadar shugaban Najeriya ta ce an baza sojoji da ƴan sanda domin kuɓutar da su.

    Sanarwar da Malam Garba Shehu ya fitar ranar Asabar ta ce an gano maɓoyar maharan har ma sun yi artabu da jami'an tsaro.

    Rundunar ƴan sanda ta ce an kashe ɗaya daga cikin maharan kuma jami'inta ɗaya ya ji rauni, yayin da ta ce sufeton janar na ƴan sandan Najeriya ya tura ƙarin jami'ai domin kuɓutar da ɗaliban.

    Ƴan Najeriya da iyayen ɗaliban na dakon sanarwa daga gwamnatin tarayya ko ta jihar Katsina game da inda aka kwana kan batun kuɓutar da ɗaliban na makarantar Kankara.

    Shugaba Buhari ya yi Allah-wadai da sace ɗaliban amma gwamnatinsa na fuskantar matsin lamba, musamman kan yadda lamarin tsaro ke ƙara taɓarɓarewa a arewacin Najeriya.

  8. Gobe Litinin za a fara yi wa Amurkawa riga-kafin cutar korona

    Mutumin da ke jagorantar aikin samar da rig-akafin annobar korona na Amurka ya sanar cewa gobe Litinin za a fara yi wa al'ummar ƙasar allurar riga-kafin.

    Janar Gus Perna ya tabbatar da cewa an fara gagarumin aikin raba riga-kafin da kamfanonin Pfizer da Bio-EN-Tech suka samar zuwa jiha 50 na Amurka.

    A ƙarshen makon da ya wuce ne hukumomi a Amurka suka amince da ingancin riga-kafin.

    Za a fara kai guda miliyan uku zuwa jihohi tsakanin Asabar da Lahadi, Gustave Perna.

    Kazalika, sun bayar da sanarwar cewa riga-kafin da kamfanin Moderna ya samar shi ma yana kan hanya da zarar ya samu amincewarsu.

    A ranar Asabar, mutum 3,309 ne suka mutu sakamakon cutar a Amurka.

  9. Har yanzu ba mu cimma wata yarjejeniya ba - Boris Johnson

    Firaministan Birtaniya Boris Johnson ya ce har yanzu "mun kasa cimma matsay a kan manyan al'amura" yayin da ake tsaka da tattaunawa a rana ta ƙarshe domin ficewar ƙasar daga Tarayyar Turai.

    Tun tuni Birtaniyar ta amince da ficewa daga ƙungiyar amma yanzu ana ƙoƙarin cimma wasu yarjejeniyoyi ne da ɓangarorin biyu za su ci gaba da amfana da juna bayan ficewar ƙasar.

    Da yake magana da manema labarai, Mista Johnson ya ce yana fatan ya ci gaba da tattaunawa da sauran shugabannin ƙasashen ƙungiyar.

    "Abin da nake ganin zai faru nan kusa shi ne mu san yadda za a yi mu cika sharuɗɗan WTO (Ƙungiyar Kasuwanci ta Duniya)," in ji shi.

  10. Sojojin Najeriya sun ce sun kashe 'yan fashi uku a Katsina-Ala

    Sojojin Najeriya sun kashe 'yan fashi uku tare da kama wasu huɗu a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala ta Jihar Benue ranar Asabar.

    Hedikwatar tsaro ta sojojin ta ce dakarunta na rundunar Operation Whirl Stroke ne suka kai hari kan sansanin miyagun da ke ƙauyukan Tomatar Ugba da Kundi, inda suka kashe uku.

    Kazaliaka, an kama wasu huɗu bayan da sojojin suka bi sahun waɗanda suka tsere.

    Daga cikin makaman da aka ƙwace daga hannun 'yan fashin akwai manyan bindiga biyu ƙirar gida da ƙarama ɗaya, babur guda biyu, injin lantarki biyu, kakin sojoji biyu da kuma tarin tabar wiwi.

    A daren Juma'a wasu da ake zargin 'yan fashi ne suka kai hari wata makarantar kwana ta maza a garin Kankara na Jihar Katsina, inda suka sace ɗaruruwan yaran da ba a san adadinsu ba.

  11. Wasanmu da Man City shi ne mafi kyau tun da na zo United - Solskjae

    Kocin Manchester United Ole Gunnar Solskjae ya ce rawar da ƙungiyarsa ta taka a wasansu da Man City a jiya Asabar shi ne "mafi kyawu" a wani wasan hamayya tun bayan da ya karbi aikin horar da ƙungiyar.

    A wasan na Old Trafford wanda bai ƙayatar ba, babu ƙungiyar da ta samu damar jefa ƙwallo a raga a filin da ake yi wa laƙabi da 'Theatre Of Dreams'.

    A fallen farko na wasan, Riyad Mahrez ya tilasta wa De Gea ture ƙwallo ɗaya da ƙwallon da Gabriel Jesus ya ɗaɗa sama da kuma yunƙurin da McTominay ya yi amma ƙwallo ta wuce shi a bakin raga.

    United ta doke City a wasa uku cikin huɗu da suka buga na baya-bayan nan, ciki har da gida da waje a Premier League.

    "Mun fi riƙe ƙwallo (a wasannin baya)," in ji Solskjaer. "Tabbas da a shekarar da ta wuce ce a Etihad da tuni mun cinye su a minti na 10 zuwa 25. Da tuni mun ci ƙwallo huɗu."

    Wannan sakamako ya sa United ta koma ta 8 a teburi, ita kuma City tana ta 9.

  12. Yau ake zaɓen kansiloli a Nijar

    A ranar 27 ga wannan watan Disamba ne kuma za a fara kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasar.

  13. An yi arangama a wurin zanga-zangar goyon bayan Donald Trump

    Dubban magoya bayan Shugaban Amurka Donald Trump da ke iƙirarin an yi musu maguɗi sun yi cincirundo a wasu biranen ƙasar har ma sun yi arangama da wasu masu adawa da su ranar Asabar.

    A birnin Washington DC, an kama mutum 20 sannan an yanki mutum huɗu da wuƙa, a cewar 'yan sanda.

    Joe Biden ya doke Mista Trump a zaɓen ranar 3 ga watan Nuwamba amma har yanzu bai yarda da shan kaye ba.

    A gobe Litinin ne ake sa ran Electoral College - wakilan zaɓe na musamman da ke zaɓen shugaban ƙasar Amurka - za su bayyana Biden a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen.

    Mista Biden ya samu ƙuri'a 306 ta wakilan fiye da ta Mista Trump guda 232 sannan ya samu ƙuri'ar game gari fiye da miliyan bakwai.

    'Yan sanda a Washington sun yi ƙoƙarin shiga tsakanin ɓangarorin masu zanga-zangar biyu, abin da ya sa suka rufe ginin Black Lives Matter bayan masu zanga-zangar adawa da Trump sun taru a wurin.

  14. Portugal za ta tallafa wa Mozambique a yaƙi da masu iƙirarin jihadi

    Portugal ta yi tayin taimaka wa kasar Mozambique a yaƙin da take yi da masu iƙirarin jihadi a arewacin ƙasar.

    Ministan Tsaron Portrugal Joao Gomes Cravinho ya ce za su taimaka wa Mozambique ta hanyar horas da sojoji da kuma taimakon kayan aiki.

    Masu iƙirarin jihadi na ƙara faɗaɗa hare-harensu a lardin Cabo Delgado, inda rahotanni ke cewa an kashe sama da mutum 200 kuma fiye da miliyan ɗaya sun rasa muhallansu cikin shekara uku da suka gabata.

    Yankin Carbo Delgado na ɗauke da iskar gas da ta kai darajar dalar Amurka biliyan 60.

  15. Buhari ya taya Anthony Joshua murnar lashe wasan dambe

    Muhammadu Buhari, shugaban Najeriya, ya taya haifaffen Najeriya kuma ɗan damben boxing, Anthony Joshua, murnar nasarar da ya yi a damben da ya doke Kubrat Pulev a daren Asabar.

    "Shugaban ya ce kare kambun IBF, WBA, da WBO da Joshua ya yi ya sa masoya wasan damben boxing a faɗin duniya da Najeriya murna," a cewar sanarwar da Femi Adesina ya fitar.

    Buhari ya bayyana zakaran damben a matsayin "mai ƙanƙan da kai da kuma tarbiyya" a lokacin da suka haɗu a birnin Landan a farkon wannan shekarar.

    Kazalika, Buhari ya yi wa Joshua fatan alheri a damben da zai gwabza da Tyson Fury nan gaba, yana mai cewa "addu'o'in 'yan Najeriya na tare da kai".

    Shi ma tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar ya ce Joshua "na ƙara ƙarfafa mana gwiwa mu 'yan Najeriya, ku jinjina wa zakara".

    Anthony Joshua ya lallasa Kubrat Pulev a gaban 'yan kallo 1,000 a filin wasa na Wembley Arena da ke birnin Landan.

  16. Buhari ya kori shugaban hukumar Neja-Delta daga aiki

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kori shugaban riƙo na hukumar kula da ci gaban yankin Neja Delta da ke kudancin ƙasar ta NDDC, Kemebradikumo Pondei.

    Sanarwar da mai taimaka wa Buhari kan kafofin yaɗa labarai, Femi Adesina, ya fitar ta ce an naɗa daraktan kuɗi na hukumar mai suna Effiong Awa a matsayin sabon shugaba.

    Adesina ya ce Awa zai ci gaba da jagorancin hukumar har zuwa lokacin da za a kammala binciken da Buhari ya bayar da umarni.

    "Wannan mataki ya zama wajibi sakamakon umarni daban-daban daga wata Babbar Kotun Tarayya ta bayar kan kwamitin riƙo na shugabancin hukumar NDDC," a cewar sanarwar.

    Buhari ya naɗa Pondei, farfesan kiwon lafiya, a matsayin shugaban hukumar a watan Fabarairu amma sai shugabancin nasa ya kasance cikin ruɗani.

    Ɗaliban Najeriya a ƙasashen waje da suka samu tallafin karatu ta hannun hukumar sun yi ƙorafi kan yadda aka yi wancakali da su da kuma sauran zarge-zargen cin hanci da rashawa a kan farfesan.

    Hakan ta sa Majalisar Tarayya ta ƙaddamar da bincike na musamman, inda ya Pondei ya yanke jiki ya faɗi yayin da yake amsa tambayoyi kan kuɗaɗen da hukumar ta kashe a lokacin dokar kullen korona - ciki har da na tafiey-tafiye zuwa ƙasashen waje.

  17. Dalilin da ke jawo ƙaruwar masu taɓin hankali lokacimn sanyi

    Shirin Amsoshin Takardunku na wannan makon ya amsa tambaya game da abin da ke jawo ƙaruwar masu taɓin hankali a loƙacin sanyi.

    Nabeela Muktar Uba ce ta gabatar da shirin.

  18. Brexit: An shiga rana ta ƙarshe a tattaunawar Birtaniya da Tarayyar Turai

    An shiga rana ta ƙarshe a tattaunawar kasuwanci tsakanin Birtaniya da Hukumar Tarayyar Turai a yuƙurin ƙasar na ficewa daga ƙungiyar Tarayyar Turai ta EU.

    Firanministan Birtaniyar Boris Johnson da Shugabar Tarayyar Ursula Von der Leyen za su yanke shawarar ko tattaunawar za ta iya ci gaba ko kuma a'a.

    Wakilin BBC ya ce kawo yanzu Birtaniya ba ta gamsu da tayin da EU ta yi musu ba kuma Fadar White House ba ta ba ta lokaci wurin bayyana rashin amincewa ba.

    A baya, duka ɓangaroran biyu sun ce ba su da ƙwarin gwiwar cewa za a cimma matsaya kan ƙulla yarjejeniyar kasuwanci ko bayan ficewar Birtaniyar.

    A kan haka ɓangaroran suka ce sun yi shirin ko-ta-kwana ko da ba a samu mafita ba daga nan zuwa ƙarshen watan Disamba.

  19. Cutar korona ta kashe mutum huɗu a Najeriya

    Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 617 da suka kamu da cutar korona a ranar Asabar.

    Kazalika ƙarin mutum huɗu sun mutu, abin da ya kawo jumillar adadin wadanda suka mutu sakamakon cutar zuwa 1,194 a kasar.

    A saƙon da ta wallafa a shafinta na intanet, NCDC ta ce an samu sabbin kamuwar ne a jiha 15 da suka haɗa da Legas (225), FCT (181), Kaduna (125),Adamawa (25), sai Nasarawa (20).

    Sauran sun hada da Kano (12), Rivers (8), Edo (4), Ekiti (4), Bayelsa (3), Ogun (3), Plateau (3), Akwa Ibom (2).

    Sai a karshe jihohin Delta da Sokoto na da mutun 1-1 kowannensu.

    Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 72,757 ne suka harbu da cutar a Najeriya, 65,850 daga cikinsu sun warke.

    A ranar 28 ga watan Fabrairu ne aka samu mutum na farko mai ɗauke da cutar a Najeriya, wani dan Italiya da ya shiga birnin Legas ranar 25 ga watan.

    Sannan a ranar 23 ga watan Maris mutum na farko ya mutu sakamakon cutar a Najeriya.

  20. Assalamu Alaikum

    Ku biyo ni Umar Mikail domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya kai-tsaye.

    Amma za mu fi mayar da hankali kan Najeriya da Nijar makwabtansu.