Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

'Gobe Litinin za a soma horas da Jam'ian Rundunar SWAT'

Wannan shafi ne da ke kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kan wasu abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Litinin idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin:

    • An yi jana'izar mutum takwas da 'yan bindiga suka kashe a Iraƙi
    • Ahmed Lawan da Gbajabiamila sun yi kira ga masu zanga-zangar #ENDSARS
    • Charlie Hebdo: Ana gudanar da zanga-zanga a Faransa kan datse kan malamin makaranta
    • Dubban mutane sun fito zanga-zangar neman sauyi a Thailand
    • Masu zanga-zangar #ENDSARS sun buɗe tashar rediyo
    • Bahrain ta ƙulla ƙawance da Isra'ila

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai

  2. An rufe rumfunan zaɓe a Guinea

    An rufe runfunan zaɓen shugaban ƙasa a Guinea mai cike da ƙalubale inda shugaban ƙasar mai shekaru 82 ke takara a karo na uku.

    An baza jami’an ƴan sanda a Conakry babban birnin ƙasar bayan shafe watanni ana mummunar zanga-zangar adawa da matakin Mista Conde ta sake tsayawa takara.

    An bayar da rahoton samun hargitsi a wasu rumfunan zaɓe, amma kuma an gudanar da zaɓen cikin lumana a mafi yawancin wurare.

    Sai dai mutane da dama ciki har da ɗaya daga cikin ƴan takara sun ce sun kasa yin zaɓen saboda matsalololin da suka shafi katin zaɓe.

    Mista Conde shi ne shugaban dimokuraɗiyya na farko da aka zaɓa a Guinea amma kuma ana ganin ya koma kama-karya.

  3. Bahrain ta ƙulla ƙawance da Isra'ila

    Jami’an Isra’ila da na Bahrain sun sanya hannu kan yarjejeniyar ƙulla dangantakar diflomasiyya tsakaninsu, a wani biki da aka gudanar a Manama babban birnin Bahrain.

    Wakilan Isra’ila – tare da rakiyar Sakataren Baitulmalin Amurka - sun tashi cikin jirgi daga Isra’ila kai tsaye zuwa Bahrain.

    Ministan harkokin wajen Bahrain da takwaransa na Isra’ila sun sanya hannu kan yarjejeniyoyi guda takwas.

    Wannan na zuwa ne bayan Isra’ila ta sasanta da Hadaddiyar Daular Larabawa a watan jiya ƙarƙashin wani kudirin Amurka na farfaɗo da hulda tsakanin Isra’ila da ƙasashen larabawa.

    Falasɗinawa dai sun yi allawadai da ƙawancen na ƙasashen Larabawa da Isra’ila wanda suka kira kamar "caka wa kai wuka ne".

  4. 'Gobe Litinin za a soma horas da Jam'ian Rundunar SWAT'

    Babban Sufeton 'yan sandan Najeriya Muhammad Adamu ya bayyana cewa gobe Litinin za a soma horas da jami'an sabuwar rundunar SWAT da aka kafa wadda za ta maye gurbin SARS.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan ƙasar, Frank Mba ya fitar, ya bayyana cewa jami'an da aka zaɓa waɗanda za su kasance cikin sabuwar rundunar matasa ne masu jini a jika kuma dukansu sun shafe aƙalla shekara bakwai suna aikin ɗan sanda.

    Hakazalika ya bayyana cewa jami'an da aka zaɓa ba su da wani tabo ko kuma tarihi na laifi da suka aikata a baya, ba kuma a taɓa samunsu da laifin take haƙƙin bil adama ba ko kuma saɓa ƙa'idar amfani da makami.

    Sanarwar ta ƙara da cewa jami'an da aka zaɓa suna da cikakkiyar lafiya da za su jure namijin horon da za a ba su.

    Za dai a soma horas da 'yan sandan ne a kwalejojin horas da 'yan sanda na Ila Oragun, da ke jihar Osun da kuma kwalejin horas da 'yan sanda ta jihar Nasarawa.

  5. Tarihin Sabon Sarkin Zazzau

  6. 'Yan adawa a Pakistan sun sa zare da Firaiministan ƙasar

    Shugabannin 'yan adawa a Pakistan sun far wa Firaiministan ƙasar da caccaka inda suke zargin gwamnatin ta Imran Khan da gaza kawo wa ƙasar ci gaba ta kowane fanni.

    Shugabannin 'yan adawan na gudanar da babbar zanga-zanga wadda ita ce ta biyu bayan kwanaki inda suke cewa firaiministan ya samu mulki a zaɓen da sojoji suka taimaka wurin yin maguɗi a 2018.

    Sai dai Mista Khan ya musanta duka zarge-zargen da suke yi masa.

    Kafafen watsa labarai sun katse jawabin da suke nunawa kai tsaye na wani daga cikin jagororin zanga-zangar yayin da yake gabatar da jawabinsa a filin zanga-zangar.

    Sun katse jawabin ne sakamakon caccakar da yake yi na gwamnati inda yake cewa sojoji ne ke juya akalar ƙasar.

  7. Masu zanga-zangar #ENDSARS sun buɗe tashar rediyo

    Masu gudanar da zanga-zangar #ENDSARS a ranar Lahadi sun ƙaddamar da wata tashar rediyo wadda ake iya kamawa ta intanet.

    Gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito cewa tashar rediyon mai suna "Soro Soke" na gabatar da shirye-shirye na wayar da kan masu zanga-zanga da kuma faɗakar da su kan yadda za a ci gaba da gudanar da zanga-zangar a faɗin ƙasar.

    Tashar rediyon ta kuma buɗe shafin Twitter inda take amfanin da shafin a matsayin wata turba ta yaɗa manufofinta.

    Soro Soke kalma ce dai ta Yarabanci wadda take nufin Yi Magana.

  8. Ali Nuhu ya yi amai ya lashe kan zanga-zangar #SecureNorth

    Fitaccen tauraron fina-finan Kannywood, Ali Nuhu, ya yi amai ya lashe sakamakon a yanzu ya shiga zanga-zangar #SecureNorth, inda a baya ya ƙi shiga zanga-zangar kan wasu dalilai nasa.

    A baya dai, dalilin da ɗan wasan ya bayar na ƙin shiga gangamin da aka shirya na jawo hankalin mahukuntan Najeriya kan rashin tsaron da arewacin kasar ke fama da shi ya janyo masa matukar suka a shafin Twitter amma duk da haka, tauraron ya shaida wa BBC cewa shi ko a jikinsa.

    Karanta cikakken labarin a nan:

  9. An ciji mai tsaron raga a gasar Faransa ta rukuni na biyu

    Ana zargin wani dan kwallo da cizon mai tsaron raga a lokacin gasar Faransa ta 'yan rukuni na biyu.

    A wasan da suka buga ranar Asabar, an bar mai tsaron ragar Valenciennes, Jerome Prior dauke da jini a kumatunsa, inda kungiyar ta zargi dan wasan Sochaux, Ousseynou Thioune da yin cizon.

    "An gartsa wa Jerome cizo a kumatunsa," Kamar yadda shugaban Valenciennes, Eddy Zdziech ya shaida wa kafar yada labarai ta AFP.

    Ga cikakken labarin a nan:

  10. Dubban mutane sun fito zanga-zangar neman sauyi a Thailand

    Dubban mutane ne suka fito zanga-zanga a Thailand inda suke buƙatar a kawo sauyi a ɓangaren siyasar ƙasar.

    An gudanar da zanga-zanga har guda biyu a Bangkok babban birnin ƙasar bayan gwamnatin ƙasar ta saka dokar haramta taruwar jama'a.

    A gwagwarmayar da aka shafe watanni ana yi, masu zanga-zangar suna buƙatar sauya yanayin gudanar da mulki na ƙasar ya bar hannun sojoji da kuma gidan sarauta.

    Firaiministan ƙasar, Prayut Chan O-Cha ya yi watsi da buƙatar 'yan ƙasar ta ya sauka daga muƙaminsa.

    An dai kama aƙalla masu zanga-zanga 50 tun daga ranar Alhamis inda kuma dubban mutane ke ƙara fitowa zanga-zangar.

  11. Charlie Hebdo: Ana gudanar da zanga-zanga a Faransa kan datse kan malamin makaranta

    An fara gudanar da zanga-zanga a biranen da ke ƙasar Faransa tun bayan datse kan wani malamin makaranta da aka yi a wani hari da ake zargin masu iƙirarin jihadi suka kai.

    Ana sa ran gudanar da babbar zanga-zanga a birnin Paris. An dai kashe Samuel Party ne a ranar Juma'a a wajen birnin na Paris.

    An kai masa harin ne sakamakon nuna wa ɗaliban da yake koyarwa wasu zane-zane na ɓatanci da aka yi ga Annabi Muhammad SAW.

    A halin yanzu dai ana binciken mutum 11 kan zargin kisan da aka aiwatar. Tuni kuma 'yan sanda suka kashe wanda ya datse kan malamin.

  12. Ahmed Lawan da Gbajabiamila sun yi kira ga masu zanga-zangar #ENDSARS

    Shugaban Majalisar Dattawan Najeriya Ahmed Lawan da kuma Kakakin Majalisar Wakilai Femi Gbajabiamila, sun yi kira ga masu gudanar da zanga-zangar #Endsars a faɗin Najeriya da su yi haƙuri su bar zanga-zangar.

    Sun bayyana haka ne bayan tattaunawa da Shugaban ƙasar Muhammadu Buhari a fadarsa da ke Abuja a ranar Lahadi.

    Ahmed Lawan ya bayyana cewa masu zanga-zangar sun gabatar da kokensu kuma gwamnati ta ɗauki mataki, lokaci ya yi da ya kamata a daina wannan zanga-zangar.

    Ya ce wannan zanga-zangar na takura wa jama'a da dama musamman masu gudanar da kasuwanci wanda hakan ke kawo cikas ga tattalin arziƙin Najeriya

  13. An yi jana'izar mutum takwas da 'yan bindiga suka kashe a Iraƙi

    Firaiministan Iraƙi, Mustafa al-Kadhimi ya halarci jana'izar mutum takwas waɗanda wasu 'yan bindiga suka kashe bayan garkuwa da su a lardin Salahuddin da ke arewacin Bagadaza.

    Mista Kadhimi ya samu tattaunawa da jami'an tsaro da ke lardin inda ya sha alwashin cewa ƙasar Iraƙi za ta ci gaba da kare mutanenta.

    Ana zaton an kuma yi garkuwa da wasu mutum huɗu a harin da 'yan bindigar suka kai kuma har yanzu babu labarinsu.

    'Yan ƙasar da dama na zargin 'yan tayar da ƙayar baya na Iraƙi waɗanda ke samun goyon baya da aikata wannan aika-aikar, inda 'yan ƙasar ke kira ga 'yan majalisa da kuma jami'ai a lardin na Salahuddin da su ɗauy mataki.

  14. Gwamna Zulum ya ayyana Litinin a matsayin ranar azumi a Borno

    Gwamnan Borno Babagana Umara Zulum ya umarci al'ummar jihar da su ɗauki azumi a gobe Litinin domin yin addu'o'in kawo ƙarshen rikicin Boko Haram.

    Gwamnan ya ayyana Litinin a matsayin rana ta biyu ta azumi a faɗin jihar ne ranar Asabar yayin da yake jawabi a wurin wani taron masu ruwa da tsaki da ya jagoranta a Maiduguri, babban birnin jihar.

    Zulum ya ce ɗaya daga cikin hanyoyin da mutane za su taimaka a yaƙi da Boko Haram ita ce, kar su shiga ƙungiyoyin 'yan bindiga sannan su riƙa taimaka wa sojoji da bayanai da kuma yin addu'o'i.

    "Bisa wannan yunƙruin ne na kirawo taro da Mai Alfarma Shehun Borno da Babban Limami da limaman masallatan Juma'a da shugabannin Kiristoci muka tattauna," in ji shi.

    "Biyo bayan wannan tattaunawa, na ayyana Litinin, 19 ga watan Oktoba a matsayin ranar azumi a karo na biyu da kuma addu'o'i a Jihar Borno.

    "Ina roƙon mu fara wannan azumi da shauƙi da jajircewa kamar na ranar 24 ga watan Fabarairun 2020."

    Gwamnan ya jaddada cewa babu hutun aiki a ranar Litinin ɗin sannan kuma ya ce babu wani taron jama'a. "Abin da ake buƙata kawai shi ne tsarkake zuciya tare da yin addu'o'i daga gidajemmu," in ji Zulum.

    Yaƙin Boko Haram ya jawo asarar ran mutum fiye da 36,000 tun daga shekarar 2009, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, wasu fiye da miliyan uku suka rasa matsugunansu - mafi yawa a Jihar Borno.

  15. Boko Haram ta kashe mutum uku, ta yi garkuwa da yara biyar a Kamaru

    Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe mutum uku tare da yin garkuwa da yara biyar a lardin arewa mai nisa na Kamaru, a cewar hukumomin yankin ranar Asabar.

    Magajin Gari Boukar Medjeweh ya shaida wa AFP cewa lamarin ya faru ne da tsakar daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma'a a ƙauyen Oudal mai nisan kilomita shida daga iyakar Najeriya, inda mayaƙan ke da sansani.

    Mutanen da aka kashe duka maza ne, su kuma yaran da aka sace 'yan tsakanin shekara uku ne zuwa 15, in ji Medjeweh.

    Shi ma Mahamat Chetima Abba, wani hakimi a yankin, ya tabbatar da harin kuma ya alaƙanta shi da Boko Haram.

    Ƙungiyoyin Boko Haram da kuma Islamic State in West Africa Province (ISWAP) sun matsa wa yankin da kai hare-hare a 'yan kwanakin nan, kamar yadda suka matsa wa garuruwan kan iyakar Najeriya da ƙasashen Chadi da Nijar.

    Jumillar mutum fiye da 36,000 ne suka rasa rayukansu sanadiyyar rikicin Boko Haram tun daga shekarar 2009, a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya, wasu fiye da miliyan uku suka rasa matsugunansu.

  16. Ba ni da hannu a zanga-zangar EndSARS – Tinubu

    Jagoran jam'iyyar APC mai mulki a Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya nisanta kansa daga zanga-zangar EndSARS da matasa suka shafe mako biyu suna yi a wasu jihohin ƙasar.

    Mai magana da yawun Tinubu, Tunde Rahman, ya faɗa cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya Asabar cewa ba daidai ba ne a ce mai gidan nasa ne ke ɗaukar nauyin zanga-zangar, kamar yadda ake yaɗawa.

    Ya ce abu ne mai wuya Tinubu ya iya ɗaukar nauyin zanga-zangar a duka jihohin da ake yi.

    "Ba zai yiwu Asiwaju Tinubu ya ɗauki nauyin zanga-zangar da ta toshe ɗaya daga cikin hanyoyin shiga da fita daga Jihar Legas ba, wadda take ɗaya daga hanyoyin samun kuɗin shiga ga gwamnatin jihar," a cewar sanarwar.

    "Kazalika, ba zai yiwu ya ɗauki nauyin zanga-zangar ba a jihohin da su kansu masu zanga-zangar ke adawa da shi."

    Haka nan sanarwar ta ce Tinubu ya aminta cewa ya kamata a rushe rundunar SARS sakamakon "lokaci mai tsawo da ta ɗauka tana cin zarafin matasa da sauran 'yan ƙasa" kamar yadda masu zanga-zangar suka buƙata.

    Sai dai ya ce ya kamata a nemi hanyoyin lumana domin gabatar da buƙatu ga gwamnati.

    Mako biyu kenan ana zanga-zangar neman rushe rundunar 'yan sanda ta SARS a Najeriya, sai dai zarce zuwa ta neman sauya salon mulki bayan Gwamnatin Tarayya ta rushe tare da maye gurbin SARS ɗin da SWAT.

  17. An sako Ali Nuhu a gaba saboda ya ƙi shiga zanga-zanga a Twitter

    Masu amfani da shafin Twitter a arewacin Najeriya sun sako tauraron fim Ali Nuhu a gaba saboda ya ƙi shiga zanga-zangar neman daƙile matsalar tsaro.

    Kusan mako guda kenan matasa 'yan Arewa na amfani da maudu'ai kamar #EndNorthBanditry da #SecureNorth da #EndInsecurity domin kira ga gwamnati ta samar da tsaro a yankin, yayin da 'yan uwansu na kudancin ƙasar ke neman rushe rundunar 'yan sanda ta SARS bisa zargin cin zarafi da kashe mutane ba bisa ƙa'ida ba.

    Ko a jiya Asabar an gudanar da zanga-zangar #EndInsecurity a Kano da Kaduna da wasu jihohin Arewa. Sai dai ba a ji ɗuriyar Ali Nuhu ba da kuma wasu manyan taurarin Kannywood.

    Cikin hira da wata kafar yaɗa labarai, Ali Nuhu ya bayyana cewa 'yan Kannywood "ba sa shiga gaba-gaba a irin waɗannan lamura saboda irin zagin da suke sha a hannun masu amfani da shafukan sada zumnta".

    Wannan cewa yake: "Ali Nuhu ya ce ba zai shiga zanga-zanga a Arewa ba saboda mutane na zaginsa. Ba zai goyi bayan mutanen da ke kallon fina-finansa ba. Ya kamata a tambaye shi, shin za mu iya kallon fim ɗinsa idan ba mu da rai?"

    Shi ma wannan cewa yake: "'Duk irin zagin da 'yan Najeriya ke yi wa Shugaba Buhari, matarsa ta shiga zanga-zangar #SecureNorth. Ali Nuhu daga Kano na cewa ba zai shiga zanga-zanga ba saboda ana zaginsa."

    Wannan kuwa kare Ali Nuhu yake yi: "Gaskiya ya faɗa muku. Ko yanzu maimakon abin da kuka saka a gaba ya yi shuhura, Ali Nuhu ne yake shuhura saboda kun dage a kan abin da kuka fi ƙwarewa a kai; zagin mutane."

    Taurarin Kannywood da mawaƙa da yawa sun shiga zanga-zangar a shafukan sada zumunta irinsu Rahama Sadau da Aminu Saira da Ali Jita da Dj Ab da Deezell da Classic.

    Sai dai ba Ali Nuhu ne kaɗai ba a ji ɗuriya ba a cikin manyan taurarin Kannywood, Hadiza Gabon da Fati Washa da Adam Zango da Hafsat Shehu, su ma ba a ji ɗuriyar tasu ba.

  18. Gwamnan Ogun ya kafa kwamitin bincike kan cin zalin 'yan sanda

    Gwamnan Jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya, Dapo Abiodun, ya kafa kwamitin da zai bincika cin zarafin da 'yan sanda suka aikata a jihar.

    Gwamnan ya naɗa mambobin kwamiti guda uku ne yayin da matasa ke ci gaba da zanga-zangar EndSARS a Ogun da wasu jihohin Najeriya.

    Kwamitocin su ne na shari'a mai suna Judicial Panel of Investigation, da na tsaro da kare haƙƙi mai suna Special Security and Human Rights Committee, da kuma na karɓar ƙorafe-ƙorafe mai suna Human Rights Complaints Office.

    Mai magana da yawun gwamnan, Kunle Somorin, shi ne ya sanar da hakan a jiya Asabar.

    Wannan ya biyo bayan umarnin da Majalisar Tattalin Arziki ta Ƙasa ta bayar ne sakamakon taron da ta yi ranar Alhamis ƙarƙashin jagorancin Mataimakin Shugaban Ƙasa Farfesa Yemi Osinbajo.

    Kwamitin shari'ar zai kasance ƙarƙashin shugabancin tsohon alƙalin Kotun Tarayya Mai Shari'a Solomon Olugbemi, yayin da Oluwatosin Ogundele za ta kasance a matsayin sakatariya.

    Daga cikin matakan da gwamnati ta ɗauka kamar yadda masu zanga-zangar neman gyara ayyukan 'yan sanda a Najeriya suka buƙata, kowanne gwamna zai kafa kwamitin jin bahasi da bincike da kuma biyan diyya ga waɗanda 'yan sanda suka ci zarafi ko kisa a jiharsa.

  19. Waɗanda suka kamu da cutar korona a Najeriya sun kai 61,307

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce adadin mutanen da annobar korona ta harba a ƙasar sun kai 61,307 bayan da aka gano ƙarin mutum 113 da suka kamu da cutar ranar Juma'a.

    A cewar NCDC, karin mutun huɗu sun mutu saboda cutar a ranar Asabar wanda yasa adadin mamatan da cutar ta kashe ya kai 1,123.

    Kazalika an samu karin wadanda suka warke daga cutar, abin da ya sa jumullar wadanda aka sallama daga asibiti ya kai 56,557.

    Jihar Legas ce ke kan gaba a yawan wadanda suka kamu da cutar, inda aka samu mutum 37, sai kuma Kaduna mai mutum 16 yayin da Ogun ke da 11.

    Jihohin Taraba na da 8 inda Rivers ke da mutum 7, sai Abuja mai mutum 6, yayin da Enugu da Neja ke da mutun 4-4, sai kuma Edo mai mutun 3.

    Delta da Imo na da mutum 2-2 kowannensu, sai kuma Benue da Kano masu mutum 1-1 da suka kamu da cutar ta korona kowannensu.

  20. Ana zaɓen shugaban ƙasa a Guinea

    Al'umma a ƙasar Guinea za su fita rumfunan zaɓe a yau Lahadi domin kaɗa ƙuri'a a zaɓen shugaban ƙasa, duk da ana tsoron barkewar rikicin ƙabilanci.

    Shugaba Alpha Conde mai shekara 82 na neman wa'adin mulki na uku bayan da ya sauya kundin tsarin mulki a watan Maris da ya ba shi damar tsayawa takarar.

    Amma hakan ya haifar da mummunar zanga-zanga da ta yi sanadin kashe mutum 50.

    Mr Conde wanda shi ne shugaban farar hula na farko a Guinea, zai fafata da 'yan takarar 11, kuma za a je zagaye na biyu idan a ka rasa wanda ya samu kashi 50 cikin 100 na kuri'un da aka kaɗa.