Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Wasu ƙasashen Musulmi sun sa 'tsauraran' matakai kan layya

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Lahadi idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da kuma wallafa a wannan shafin

    • Trump zai toshe TikTok a Amurka
    • Muna cikin tashin hankali a Borno – Shehun Borno
    • Rikicin ƙabilanci ya yi sanadin mutuwar mutum 15 a Darfur
    • Cikakkiyar hirar BBC da Malam Mamman Daura
    • Giya mara rajista ta kashe sama da mutum 80 a Indiya
    • Za a buɗe masallatai da coci-coci a Legas

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labaran da ma wasu muhimmai.

  2. Wasu ƙasashen Musulmi sun sa 'tsauraran' matakai kan layya

    Kasashe da dama da ke bikin Sallar Layya sun bijiro da tsauraran matakai na sanya iyaka kan yawan dabbobin da za a yanka da kuma yadda za a yi yankan a yunƙurin ɗaukar matakan faɗawa hatsarin watsuwar cutar korona.

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta fitar da sabbin ka'idoji tana gargaɗin jama'a da su yi taka tsantsan yayin yanka dabbobi layya.

    A Indonisiya, ƙasar da ta fi yawan musulmi a duniya, masallatai da dama sun dakatar da yanka dabbobi, sannan an samu karuwar sayen awaki masu rai da kuma nama ta internet. A Pakistan da Indiya da Bangaladash ma an samu karuwar cinikin dabbobi ta intanet.

    A gabas ta tsakiya kuma an daura alhakin ganin karancin dabbobi a kasuwanni kan dokar kulle, da tsarin nisantar jama'a da kuma tsabar tsadar dabbobin .

  3. Facebook ya toshe shafukan magoya bayan Shugaban Brazil

    Kamfanin Facebook ya toshe shafuka da dama na masu goyon bayan Shugaban Brazil Jair Bolsonaro.

    Ana binciken mutanen ne a halin yanzu bisa zargin yaɗa labaran ƙarya kan alƙalan Kotun Ƙoli ƙasar.

    A ranar Juma'a, Kotun Kolin ƙasar ta ci kamfanin Facebook tarar kuɗi sakamakon ƙin bin hukuncin da ta yanke.

    Sai dai kamfanin ya ce matakan da kotun ta ɗauka na da tsauri matuƙa kuma matakan na barazana ga 'yancin bayyana ra'ayi a Brazil.

  4. Dubban mutane na zanga-zangar adawa da dokokin korona a Jamus

    Dubban mutane ke zanga-zanga a Berlin babban birnin ƙasar Jamus inda suke nuna ƙin amincewar su kan dokokin korona.

    Waɗanda suka halarci zanga-zangar na ta waƙe-waƙe da pito yayin zanga-zangar wadda suka yi da bada tazara a tsakani inda mutane kaɗan suka saka takunkumi.

    Wakilin BBC da ke a Berlin ya ce masu zanga-zangar na da wani ra'ayi na daban inda kwata-kwata ma ba su yarda akwai cutar korona ba, amma a cewarsa akwai wasu daga cikinsu waɗanda sun yarda da cutar amma kawai suna adawa da matakin da gwamnatin Jamus ɗin ta ɗauka na yaƙi da cutar korona.

    A ranar Juma'a dai sama da mutum 900 suka kamu da cutar a ƙasar inda kuma mutum bakwai suka mutu.

  5. Za a buɗe masallatai da coci-coci a Legas

    Gwamnan jihar Legas Babajide Sanwo-Olu, ya bayar da damar buɗe wuraren ibada a jihar daga 7 ga watan Agusta.

    Gwamna Sanwo-Olu ya bayyana hakan yayin bayar da bayanai kan cutar ta korona a gidan gwamnatin jihar da ke Marina.

    Ya bayyana cewa masallatai za su iya buɗewa ranar Juma'a 7 ga watan Agusta, sai kuma coci ranar Lahadi 9 ga watan Agusta.

    Jihar Legas ce dai kan gaba a yawan masu ɗauke da cutar korona a Najeriya.

    Tun a watan Maris aka bayar da umarnin rufe wuraren ibadu a jihar a yunƙurin daƙile yaɗuwar cutar

  6. Mutum 10 sun mutu a hatsarin jirgin ruwa a Legas

    Rundunar 'yan sanda reshen jihar Legas a ranar Juma'a ta tabbatar da mutuwar mutum 10 sakamakon hatsarin jirgin ruwa da ya faru a ranar Laraba kusa da Unguwar Apapa da ke jihar.

    Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito 'yan sandan ƙasar inda suka ce akwai mutum uku sun ɓace ba a gansu ba, amma an samu nasarar ceto mutum biyar cikin fasinjoji 18 da ke jirigin ruwan.

    An ce jirigin ruwan ya taso ne daga Kirikiri a hanyarsa ta zuwa Badagry wanda ya kuma jirkice kusan misalin 5:00 na yamma.

    Ana dai yawan samun irin wannan hatsarin na jirgin ruwa wanda kuma akasari ana alaƙanta hatsarin ne da yawan lodi da ake yi wa jirigin ruwan ko kuma kwale-kwale.

  7. Giya mara rajista ta kashe sama da mutum 80 a Indiya

    Jami'ai a arewacin jihar Punjab ta Indiya sun bayyana cewa sama da mutum 80 suka mutu sakamakon shan barasar da aka yi ba bisa ƙa'ida ba.

    A ranar Asabar, 'yan sanda a ƙasar sun kai samame fiye da sau 100 inda suka ƙwace ɗumbin barasar da aka yi ba bisa ƙa'ida ba da kuma kama waɗanda ake zargi.

    A ƙasar ta Indiya dai, babu wadataciyyar giya a shaguna sakamakon dokar kulle.

    Ko a wannan makon nan sai da mutum tara suka mutu a Indiya bayan sun sha man wanke hannu wanda ake kira sanitiza mai ɗauke da sinadarin sa maye.

  8. Cikakkiyar hirar BBC da Malam Mamman Daura

  9. Wani matashi ya ci ɗan karen duka kan jigilar naman shanu a Indiya

    Wani matashi ya sha ɗan karen duka a Indiya sakamakon zarginsa da wasu mutane suka yi kan jigilar naman shanu.

    A halin yanzu, mutumin na asibiti inda yake jinya da kuma karɓar magani.

    Gungun mutanen dai sun bi motarsa a daidai lokacin da ya kama hanyar Gurugram da ke Haryana yayin da yake ɗauke da naman a motarsa.

    A ƙarshe dai sun samu nasarar ciro shi daga motar inda suka lakaɗa masa duka.

    Bidiyon harin da suka kai masa na yawo a kafafen sada zumunta, 'yan sanda kuma sun yi rajistar wannan lamari a matsayin laifi, amma har yanzu ba su kama kowa ba.

    Mutumin da ya sha dukan ya musanta laifin da ake zarginsa da shi inda ya ce naman ɓauna ne ya ɗauko.

    Masu bin addinin Hindu a Indiya na girmama Shanu inda a wasu sassan na Indiya ba a cin naman.

  10. Rikicin ƙabilanci ya yi sanadin mutuwar mutum 15 a Darfur

    Akalla mutum 15 ne aka kashe, aka kuma raunata 20 yayin wata arangama a yankin Darfur da ke yammacin Sudan.

    Gwamnan kudancin jihar Darfur Hamed al Tigani, ya bayyana cewa an shafe kwana biyu ana gwabza faɗa tsakanin ƙabilun Arab Taaisha da kuma Falata.

    Sababin rikicin ya samo asali ne kan batun wata gona da ake rigima a kanta.

    A makon da ya gabata ne Firaiministan ƙasar Abdallah Hamdok ya sanar da cewa za a kai wata runduna ta musamman ta haɗin gwiwa a Darfur ɗin domin kawo ƙarshen rikici.

    Ya ce rundunar za ta haɗa da sojoji da 'yan sanda da kuma dakarun Rapid Support Forces - wata ƙungiya da ta yi ƙaurin suna a baya kan tayar da ƙayar baya da ake kira Janjaweed wadda ake zargi da aikata muggan laifuka a baya.

    A makon da ya gabata ne dai 'yan tayar da ƙayar baya a ƙasar ta Sudan suka kashe farar hula 60 a yankin na Darfur.

  11. Muna cikin tashin hankali a Borno – Shehun Borno

    Mai Alfarma Shehun Borno, Alhaji Abubakar Ibn Umar Garbai Elkanemi ya koka cewa shugabanni da mazauna Jihar Borno ba su tsira ba daga hare-haren 'yan bindiga.

    Basaraken yana magana ne kan harin da aka kai wa tawagar Gwamna Babagana Umara Zulum yayin da ya kai wa Gwamnan ziyarar Sallah a fadar gwamnati da ke birnin Maiduguri.

    A ranar Laraba ne aka kai wa jerin motocin gwamnan hari a garin Baga na Ƙaramar Hukumar Kukawa lokacin da yake kan ziyara a yankin.

    An ga Gwamna Zulum a wani bidiyo lokacin da harin ke faruwa yana zargin sojojin da gazawa sannan daga baya ya zarge su da yi masa zagon ƙasa.

    "Idan har za a kai wa babban mutum irin wannan hari, to ina tabbatar muku cewa babu wanda ya tsira a jihar nan," in Shuhun Borno, kamar yadda mai bai wa shawara kan kafofin yaɗa labarai Isa Gusau ya rawaito.

    Ya ci gaba da cewa: "Mai girma gwamna ba mu ji daɗin abin da ya faru ba a Baga kuma abin tausayi ne. Yanayin ƙara munana yake."

    Elkanemi ya nemi jama'a da su ci gaba da addu'a domin kawo ƙarshen matsalar Boko Haram, wadda ta jawo asarar rayukan mutum fiye da 20,000 a cewar Majalisar Ɗinkin Duniya.

  12. Mahajjata na gudanar da Jifan Sheɗan

    Tun misalin ƙarfe 1:00 na dare mahajjata suka fara isa filin Jamrah wato Jifan Sheɗan a ci gaba da ibadar aikin Hajjin bana.

    Wani mahajjaci mai suna Rayyan Hamza Abdallah ya faɗa BBC cewa hukumomi sun ba su duwatsu na musamman domin yin jifan sheɗan.

    An ba su duwatsun ne bayan an yi musu feshin magani a matsayin matakan hana yaɗuwar cutar korona da aka ɗauka a lokacin aikin Hajjin.

  13. Idan kun nemi aikin ɗan sanda a Najeriya...

    Rundunar 'yan sandan Najeriya ta buƙaci duk waɗanda suka nemi aikin ɗan sanda da su sake ziyartar shafinta na intanet daga ranar Juma'a 31 ga watan Yuli domin sabunta bayanansu.

    Rundunar ta bayyana haka ne a watan sanarwa da ta wallafa a shafukanta na zumunta.

    Abubuwan da za a yi idan an shiga shafin sun haɗa da:

    • Shigar da lambar katin ɗan ƙasa ta National Identification Number (NIN)
    • Bayar da ƙrin bayanan da aka nema
    • Saka kwafin takardun sakandare da takardar haihuwa da shaidar inda kuka fito wato Certificate of Origin
    • Fito da kwafi na bayanan da kuka bayar tare da kiyaye lambar fom ɗin
    • Sannan a sauke tare da yin kwafin fom ɗin mai tsaya muku
    • Adireshin da za a je www.policerecruitment.gov.ng
  14. Mutum fiye da 57,000 sun kamu da korona a Indiya cikin kwana ɗaya

    Gwamnatin Indiya ta ce an samu ƙrin fiye da mutum 57,000 da suka harbu da cutar korona a cikin sa'a 24 da suka wuce - mafi yawan adadi kenan tun bayan ɓullar cutar.

    Wannan ce rana ta uku a jere da ake samun sama da mutum 50,000 da ke kamuwa da cutar, yayin da adadin ke ci gaba da hauhawa a kullum.

    Maharashtra - yankin da ke ƙunshe da Mumbai - har yanzu shi ne cutar ta fi wa ƙamari.

    Sai dai sauran yankuna da suka haɗa da Andhra Pradesh da Telangana da Assam.

  15. Trump zai toshe TikTok a Amurka

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai haramta amfani da manhajar dandalin TikTok a ƙasarsa.

    Ya faɗa wa manema labarai cewa zai saka hannu kan wata dokar ɓangaren zartarwa nan ranar Asabar.

    Jami'an tsaron Amurka sun bayyana fargabvar cewa za a iya amfani da manhajar, wadda kamfanin ByteDance na China ya mallaka, wurin satar bayanan Amurkawa.

    TikTok ya ƙaryata zargin cewa gwamnatin China ce ke iko da shi kuma ba ya bai wa gwamnatin bayanan masu amfani da shi.

    Dandalin wanda ake ɗauka tare da yaɗa gajeriun bidiyo, na da masu amfani da shi miliyan 80 duk wata a Amurka kuma rufe shi ba ƙaramar asara ba ce ga kamfanin.

    "Game da TikTok, za mu toshe shi a Amurka," in ji Trump, yayin da yake magana a jirgin sama.

  16. Cutar korona ta kashe mutum ɗaya a Najeriya ranar Sallah

    Yawan masu cutar korona a Najeriya ya kai 43,151 bayan sake gano mutum 462 da suka kamu da korona ranar Juma'a.

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa ta nuna cikin alƙaluman da take fitarwa kullum cewa maras lafiya ɗaya ya mutu sakamakon cutar korona cikin sa'a 24.

    Yawan mutanen da suka rasu sakamakon wannan annoba a Najeriya 879.

    Sai dai mafi yawa cikin adadin mutanen da cutar ta sake shafa, sun fito ne daga Abuja, babban birnin ƙasar da yawan mutum 93, kwana guda bayan wasu 96 sun kamu.

    NCDC ta kuma nuna cewa masu korona 295 ne suka warke kuma har aka sallame su don komawa gidajensu a ranar Juma'a.

    Hakan ya nuna har yanzu akwai masu cutar korona 22,707 da ke kwance suna jinya a cibiyoyin kwantar da masu cutar a sassan Najeriya.

  17. An gurfanar da wadanda suka yi wa shafukan Twitter na manyan mutane kutse a kotu

    Masu gabatar da kara a Amurka sun tuhumi wasu mutane uku da hannu a gagarumin kutsen da aka yi wa wasu fitattun yan kasar mako biyu da suka gabata.

    Ana zargin wani matashi dan shekara 17 daga jihar Florida da jagorantar kutsen da aka yi wa shafin Twitter na dan takarar shugaban Amurka Joe Biden, da na tsohon shugaban kasar Barrack Obama, da hamshakin dan kasuwar nan Jeff Bezzos da mawaki Kanye West.

    Masu satar bayanan sun nemi wadanda ke bibiyar fitatattun mutanen su aika musu da kudin Internet na Bitcoin, bisa alkawarin ninka musu duk abin da suka aika.

    Wakilin BBC ya ce kamfanin Twitter ya yi karin haske a kan yadda aka yi kutsen, in da ya ce wasu ma'aikatansa aka yaudara da kiran waya har ta kai ga sun bayar da bayanan shafukan wadanda aka yi wa kutsen, da shi ne kuma suka yi amfani wajen cimma manufarsu.

  18. Assalamu Alaikum

    Umar Mikail ke yi muku barka da shigowa shafin labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabta da sauran sassan duniya.

    Da fatan za ku kasance da mu daga yanzu har zuwa daren yau.