Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Masu kamuwa da korona za su rika kai 500,000 a Amurka a Kullum

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya and Nabeela Mukhtar Uba

  1. Rufewa

    A nan ne muka kawo karshen labarai da rahotannin da muke kawo muku kai tsaye a wannan shafin.

    Sai ku kasance da mu gobe domin karanta wasu sabbin labarai da rahotonnin da muke kawo muku.

    Amma yanzu a madadin abokan aiki aina Nasidi Yahaya da Nabeela Mukhtar ni Buhari Muhammad Fagge ke cewa mu kwana lafiya.

  2. Masu kamuwa da korona za su rika kai 500,000 a Amurka a Kullum

    Jagoran yaƙi da annobar Korona a Amurka Anthony Fauci ya ce idan ba a yi hattar ba za a fara samun masu kamuwa da cutar sama da dubu dari a ko wacce rana a kasar.

    Dakta Fauci ya ta'allaka karuwar yaduwar cutar da cakuduwar jama'a kuma ba tare da sun saka takunkumin fuska ba, da kuma rashin kiyaye suaran dokoki.

    Birnin New York da ya sha wahala sosai a zagayen farko na annobar ya saka dokar killace jama'a ta mako biyu, ganin yadda annobar ke ci gaba a sauran jahohi.

  3. Sama da mutum Miliyan daya ne suka rasa muhallansu a Jamhuriyar Demokradiyar Congo

    Majalisar Dinkin Duniya ta ce sama da mutum miliyan daya ne suka rasa muhallansu saboda rikici, a Jamhuriyar Demokradiyar Congo a cikin watanni shida.

    Hukumar da ke kula da yan gudun hijira ta majalisar ta ce an samu hare hare a lokuta daban-daban a gabacin Ituri da kudancin da kuma arewacin Kivu a tsawon lokacin.

    Hukumar ta ce akwai rahotannin kisan wadanda suka yi karfin halin komawa gidajensu da fyade da kuma sata.

  4. Shugabanni sun taru don tattauna rikicin yankin Sahel

    Shugabannin kasashen Yammacin Afrika biyar tare da shugaban Faransa Emmanuel Macron sun hadu domin tattauna kokarin da suke na yaƙi masu jihadi a yankin Sahel ya zuwa yanzu.

    Lokacin da ya karasa wajen taron a Nouakchott babban birnin kasar Mauritanian, Macron ya matukar yabawa shugababbin tare da bayyana kokarin a matsayin wata nasara da aka samu a 'yan watannin nan, wadda ta hadar da kashe wani shugaban mayakan.

    A yan shekarun nan aikin kungiyoyin masu ikirarin jihadin na karuwa a yankin Sahel, duk da zuwan dakarun wanzar da zaman lafiya na Faransa.

    Dubban soji da fararen ne ake kashewa a kusan ko wacce rana a hare-haren da ake kai wa yankin.

  5. Gadar da ta hada jihohin Filato da Taraba ta rufta

    Rahotanni daga jihar Filato a Najeriya na cewa wata babbar gada da ta hade jihar da makwabciyarta jihar Taraba ta ruguje sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya.

    Gadar wacce ke tsakanin yankunan Wase da Langtang da ke jihar ta Filato ta kasance wata babbar mahada tsakanin jihohin Filato da Taraba, inda a kullum dimbin mutane ke zirga-zirga ta tattalin arziki da zamantakewa. Lamarin ya sanya harkoki sun tsaya cak.

    Gwamnan jihar ta Filato Simon Lalong wanda ya ziyarci gadar da ta karye, ya jajanta wa al’umomin yankin kana ya yi alkawarin kai masu dauki.

    Gwamnan wanda ya kai ziyarar a ranar Talata, ya ce ko da ya ke wannan hanyar ta gwmanatin tarayya ce, to amma gwamnatin jihar za ta yi bakin kokarinta don ganin an dauki matakin sake gina gadar.

    Ya shaida wa jama’ar yankin da kuma sarakunan gargajiya a yayin ziyarar, cewa a mataki na wucin gadi, yanzu hukumomin jihar za su samar da jiragen ruwa ko kwale-kwale da za su taimaka wajen tsallakawa da matafiya tsakanin jihohin biyu.

    Mista Lalong ya kara da cewa gwamnatin jihar za ta sanar da gwamnatin tarayya domin kai dauki na gyara gadar da ma hanyar baki daya.

  6. Korona ta ɓulla a gidan yari a Rwanda

    Rwanda ta ba da rahoton samun masu cutar korona 72 a wata cibiya da 'yan sanda ke tsare mutane, cikin sabbin adadin masu kamuwa da cutar a kullum, wanda ya kai yawan masu cutar a kasar 1,000.

    Wannan ne karon farko da aka samu bullar cutar a gidan yari a Rwanda.

    Jami'an lafiya sun ce wadanda suka kamu na da alaka da wadanda aka gano na dauke da cutar a gabacin kasar.

    A makon jiya ne, hukumomin Rwanda suka kara tsawaita dokar kulle da mako biyu a wani bangare na babban birnin kasar Kigali, bayan gano wasu gwamman masu cutar.

    Kusan rabin masu cutar a Rwanda a wannan watan ne aka same su.

    An fara wani gangamin gwaji a fadin kasar a makonni biyun da suka gabata.

  7. An tumbuke butun-butumin basarake kan harbe mawaki

    Masu zanga-zanga a Habasha na ci gaba da nuna fushi kan harbe fitaccen mawakin nan da aka yi, sun ruguza butun-butumin Yarima Ras Makonnen Wolde Mikael -wanda shi ne mahaifin Haile Selassie sarki na karshe a kasar Habasha.

    Butun-butumin da ke gabacin birnin Harar ya nuna Ras Makonnen, wani dakare da ke da muhimmanci yana zaune kan doki, wanda kuma tsohon gwamnan lardin Harar a karni na 19, lokacin mulkin Menelik II.

    An ta nuna hotonan abin da ya faru a shafin Facebook yadda ake janyo butun-butumin a kasa daga inda aka kafa shi.

  8. Mawakin da aka harbe a Ethiopia

    Mawakin nan da aka harbe a Ethiopia Hachalu Hundessa ya fi karfin a kira shi mawaki kawai ko kuma mai nishadantarwa.

    Wani tauraro ne da ke nuna matsayin mutanen Oromo da suke kukan yadda aka mayar da su saniyar ware a bangaren siyasa da tattalin arziki karkashin gwamnatin kasar mai ra'ayin rikau.

    A daya daga cikin shahararrun wakokinsa, ya yi waka " kar ka jira taimako ya zo maka bdaga waje wani mafarki da ba zai taba zama gaskiya ba. Farka, shirya dokinka domin tunkarar rikici, kai ne kake kusa da fada."

    An kulle mawakin a gidan yari na tsawon shekara biyar, lokacin yana shekara 17 saboda shiga zanga-zanga da ya yi.

    Sa'annin shi da yawa sun tsere daga kasar don gudun dauri irin wanda aka yi masa, amma shi ya zauna a kasar yana karawa matasa kwarin gwiwar neman na kai.

  9. Gwamnatin Kaduna ta kafa kwamiti kan rikicin Zangon-Kataf

    Gwamnatin jihar Kaduna da ke arewacin Najeriya ta kafa wani kwamiti da zai yi nazarin rahotanni da aka gabatar da a kan rikicin Zangon-Kataf, domin ya ba ta shawara kan matakan da za ta dauka da nufin magance rikicin.

    Gwamnatin ta kafa kwamitin ne sakamakon rikicin da ake yawan samu a yankin.

    Majalisar zartarwar jihar Kaduna ce ta amince da kafa kwamitin mai mutum 8, wanda zai yi nazarin wasu rahotanni da wasu kwamitoci suka gabatar a baya, ciki har da rahoton da kwamitin bincike, wanda mai shara`a Rahila Cudjoe ta jagoranta ya gabatar a kan rigingimun da aka yi da aka yi a Zangon Kataf a watan Fabrairu da watan Mayun 1992.

    Kazalika kwamitin zai duba rahoton da kwamitin sulhu, wanda Air Vice Marshal Usman Muazu ya gabatar, shi a ma a kan rikicin Zangon Kataf din a shekarar 1995.

  10. Coronavirus: An dage gasar cin kofin Afirka

    Hukumar kwallon Kafa ta Afirka ta sanar da dage gasar cin kofin Afirka ta 2021 zuwa Janairun 2022 sakamakon annobar korona.

    A baya an tsara gudanar da gasar cikin watan Janairun shekarar 2021.

    Haka ma gasar cin kofin nahiyar Afirka ta 'yan wasan da ke taka-leda a gida wato CHAN da aka shirya yi cikin watan Aprilu, a yanzy za a gudanar da ita cikin Janairun 2021.

    Za dai a gudanar da wasannin a Kamaru.

  11. Gwamnan jihar Ondo Akeredolu ya kamu da cutar korona

    Gwamnan jihar Ondo da ke kudu maso yammacin Najeriya Rotimi Akeredolu ya kamu da cutar korona.

    Gwamnan ya bayyana haka ne a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Talata.

    A cewarsa, zai killace kansa tsawon wani lokaci, ko da yake ya ce zai ci gaba da gudanar da aikinsa na gwamna.

    Ya yi kira ga mutane su yi masa addu'ar samun sauki.

    Akeredolu shi ne gwamna na biyar da ya kamu da cutar korona a Najeirya.

    Gwamnonin sun hada da Nasir El-Rufai na Kaduna, Bala Mohammed na Bauchi, Seyi Makinde na Oyo, da Okezie Ikpeazu na Abia.

  12. Ana gangamin neman sake fasalin siyasa a Sudan, Catherine Byaruhanga BBC News, Kampala

    Dubban mutane na gudanar da gangami a birane da garuruwa a sassan Sudan don neman sauye-sauye a siyasar kasar.

    Kungiyoyin farar hula sun ce sun shirya zanga-zangar domin ganin an cimma muradan juyin juya halin da ya kai ga hambarar da mulkin Omar al-Bashir.

    An jibge jami'an tsaro a Khartoum, babban birnin kasar da garuruwan da ke makwabtaka da kuma wasu mahimman tituna da ke kaiwa ga hedikwatar rundunar sojin kasar.

    Dandazon mutane sun taru suna rera wakoki rike da alluna.

    Sai dai akwai fargabar cewa zai yi wuya a iya cimma burin sake fasalin siyasa da mulkin farar hula a kasar.

  13. Hotunan taron kaddamar da aikin shimfida bututun iskar gas mai nisan kilomita 614 a Najeriya

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya halarci taron kaddamar da katafaren aikin shimfida bututun isakar gas da zai hada kudanci da arewacin kasar mai nisan kilomita 614.

    Aikin zai soma ne daga Ajaokuta ya bi ta Kaduna sannan ya wuce Kano.

    An gudanar da taron ta intanet a fadar shugaban da ke Abuja, babban birnin kasar kamar yadda mai bai wa shugaban shawara kan kafafen sada zumunta, Bashir Ahmad ya wallafa a Twitter.

  14. Minti Daya Da BBC Na Rana

  15. Shugaban Congo ya yi fatali da sauyin da zai yi wa bangaren shari'a a kasar illa

    Shugaban Jamhuriyar Dimokradiyyar Congo Felix Tshisekedi ya sha alwashin kin amincewa da duk wasu gyare-gyare da za su shafi ikon cin gashin kan bangaren shari'a.

    Shugaban ya ce ba zai goyi bayan "gyaran fuskar da zai yi wa tsare-tsaren bangaren shari'a illa ba".

    Akwai takun saka kan shawarar karawa ma'aikatar shari'a karfin ikon game da tuhumar masu manyan laifuka.

    A makon da ya gabata, ministan shari'a ya shiga hannun hukuma na wani dan lokaci lamarin da ya sa Firaministan yin barazanar yin murabus.

    Shugaba Tshisekedi ya kulla kawance da tsohon shugaba Joseph Kabila wanda ke rike da madafun iko sakamakon rinjaye da yake da shi a majalisar dokoki da kuma ikon da yake da shi da yawancin ma'aikatun majalisar ministocin da kuma ofishin firaminista.

  16. COVID-19: Za a janye dokar hana fita a Senegal

    Shugaban Senegal Macky Sall ya ce za a janye dokar hana fita da aka sanya a kasar sakamakon bullar cutar korona daga yau Talata.

    Cikin jawabin da ya yi ta talbijin, shugaban ya kuma sanar da bude tashoshin jiragen sama daga 15 ga watan Yuli amma tare da sanya tsauraran matakan kariya.

    Mr Sall ya kuma yi gargadin cewa ci gaban tattalin arzikin zai kasance cikin tafiyar hawainiya daga kashi 6.8 cikin 100 zuwa kashi 1.1 cikin 100 saboda illar da annobar korona ta haifar.

    Ya yi kira ga mutane su koma gudanar da harkokinsu kamar yadda suka saba domin tada komadar tattalin arzikin kasar.

    Ma'aikata za su fara aiki daga karfe 8:00 na safe zuwa karfe 5:00 na yamma amma wuraren shakatawa za su ci gaba da zama a rufe.

    Haka nan za a ci gaba da rufe kasuwanni sau daya a sati domin tsaftace su. Sanya takunkumin fuska kuwa dole ne a bainar jama'a da ofisoshi da tashoshin mota da shaguna.

    A yanzu haka shugaban na killace na tsawon makwanni biyu bayan ya yi mu'amala da wani da ya harbu da korona. Killacewar za ta zo karshe ne a mako mai zuwa.

    Ya zuwa yanzu kasar ta Senegal ta tabbatar da mutum 6698 da suka kamu da cutar, 108 kuma sun mutu.

  17. Coronavirus: EU za ta bar matafiya daga kasashe 14 shiga yankin

    Kungiyar Tarayyar Turai ta sanar da kasashe 14 da al'umominsu za su iya shiga yankin na Turai daga 1 ga watan Yuli duk da annobar korona amma ban da al'umar Amurka da Brazil da China.

    Kasashen da kungiyar EU ta ambata sun hadar da Australia da Canada da Japan da Morocco da kuma Koriya ta Kudu.

    EU a shirye take ta sanya China cikin kasashen da za su iya shiga yankin idan gwamnatin ta China ta yi tayin makamanciyar yarjejeniyar ga matafiya na EU, kamar yadda jakadu suka bayyana.

  18. Labarai da dumi-dumi, An kama 'yan China da suka kulle 'yan Najeriya tsawon wata hudu a Abuja'

    Rundunar 'yan sandan Najeriya ta ce ta kama wasu 'yan kasar China biyu bisa zargin kulle wasu 'yan Najeriya inda suka kwashe wata hudu suna tursasa musu yin aiki a otal dinsu.

    Mutanen sun kwashe tsawon lokaci suna yin aikau a otal din na 'yan China da ke unguwar Jabi a Abuja, babban birnin kasar, amma ba a hana su shiga da fita ba sai watanni hudu da suka wuce lokacin da annobar korona ta yawaita a kasashen duniya.

    Rundunar ta shaida wa BBC cewa sun kama 'yan China ne bayana an kai musu tsegumin cewa sun tsare 'yan Najeriya goma a otal din ba bisa ka'ida ba.

    Daya daga cikin 'yan Najeriyan da aka kulle ta shaida wa BBC cewa 'yan Chinan sun hana su fita daga otal din ne saboda tsoron kada su kawo musu cutar korona.

    Sai dai rundunar 'yan sanda Najeriya ta ce za ta yi bincike a kan lamarin sannan ta dauki matakin da ya dace.

  19. Manchester City za ta duba yiwuwar dauko dan wasan Aston Villa Jack Grealish, mai shekara 24, idan Bayern Munich ta sayi dan wasan Jamus Leroy Sane, mai shekara 24. An ce ita ma Manchester United tana zawarcin dan wasan na Ingila. (Telegraph)

    A shirye Chelsea take ta dauko dan wasan Manchester United Angel Gomes. Kungiyoyin kasashen waje da dama suna zawarcin dan wasan na Ingila dan shekara 19. (Independent)

    Kazalika Manchester United tana son dauko Grealish domin maye gurbin Gomes. (Express)

    Newcastle da Arsenal suna cikin kungiyoyin Gasar Firimiya da ke son sayo dan wasan Wolfsburg dan kasar Netherlands Wout Weghorst, mai shekara 27, a kan euro 35m. (Bild - in German).

  20. Majalisar Dattawan Gabon ta haramta auren jinsi ɗaya

    Majalisar Dattawan Gabon ta kada kuri'a da babbar murya ta haramta auren jinsi daya, mako guda bayan takwararta ta wakilai ta amince da kudurin auren jinsi dayan.

    Idan shugaban kasar ya sanya hannu a kan dokar amincewa da auren na jinsi daya, Gabon za ta kasance daya daga cikin kasashe kalilan na Afirka da suka yarda da irin wannan doka.

    Fitattun 'yan siyasa da dama, da shugabannin addinin Kirista da na Musulunci, sun bayyana matukar bacin ransu kan batun, wanda suka ce wani yunkuri ne da kasar take yi na zama 'yar-koren kasashen waje da ke ba ta tallafi.

    A bara, kasar ta haramta luwadi sannan ta ayyana hukuncin daurin wata shida ko cin tara kan duk wanda aka samu da laifin luwadi .

    Masu auren jinsi daya sun rika buya saboda wannan doka.

    Kasashen Afirka da dama sun ayyana hukuncin dauri kan masu auren jinsi daya, wasu ma ana yin barazanar kashe su.