An kashe sojojin Burundi 20 a rikicin kan iyaka
Rahotanni daga gabashin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo sun ce an kashe sojojin Burundi aƙalla 20 a fafutukar ƙwace garin Kamanyola, inda Congo da Burundi da kuma Rwanda suka yi iyaka.
Mayaƙan M23 sun ƙwace iko a garin, inda suka fatattaki dubban dakarun Congo masu samun goyon bayan sojin Burundi.
Faɗan ya tilastawa fararen hula da dama barin yankin zuwa Rwanda, kwanaki bayan yarjejeniyar zaman lafiya da Amurka ta jagoranci ƙullawa tsakanin Rwanda da Congo.
Rahotanni sun ce lamarin ya ƙazance sosai.