Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

KAI TSAYE, Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 01/08/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Asabar 01 ga watan Agustan 2026

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Trump ya musanta zargin Iran da kutse kan tsarin samar da ruwa a Minnesota
  • Iran ta ce za ta rufe mashigar Hormuz idan Amurka ta ci gaba da kai hare-hare
  • Farashin mai ya ƙaru saboda fargabar cikas ga jigilar mai ta Mashigar Hormuz
  • Masu ba Trump shawara sun nuna adawa da shirin kai sabbin hare-hare kan Iran

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Sojojin Najeriya sun kama mutum shida kan zargin taimakawa ISWAP a Borno

    Rundunar sojin Najeriya ta ce dakarunta na Operation Hadin Kai sun kama mutum shida da ake zargi da taimaka wa mayaƙan ISWAP wajen gudanar da ayyukansu a Damasak da ke Jihar Borno.

    A cewar rundunar, an kama mutanen ne a ranar 27 ga Yulin 2026 bayan wasu bayanan sirri sun nuna cewa suna taimaka wa ƙungiyar wajen samar da kuɗaɗe ta hanyar saye da sayar da shanu a kasuwannin Gubio, Damasak da Ajuwango.

    Sojojin sun ce sun ƙwace makamai da mota da kuma kuɗi Naira 317,950 daga hannun waɗanda ake zargin.

    Rundunar ta bayyana cewa waɗanda aka kama na ci gaba da fuskantar bincike, tana mai jaddada aniyarta ta ci gaba da lalata hanyoyin samar da kuɗi da kayan aiki ga ƙungiyoyin masu tayar da ƙayar baya.

  2. Masu ba Trump shawara sun nuna adawa da shirin kai sabbin hare-hare kan Iran

    Rahotanni daga kafofin watsa labarai ta CBS da Wall Street Journal sun ce wasu masu ba shugaban Amurka Donald Trump shawara sun nuna adawa da wani shirin da ake zargin Amurka da Isra'ila na yi na kai sabbin hare-hare kan cibiyoyin makamashi a Iran.

    Rahotannin sun ce an tattauna shirin a wani taron majalisar ministocin Trump da aka gudanar a Camp David, inda wasu daga cikin masu ba shi shawara na siyasa suka yi watsi da batun ƙaddamar da sabon farmakin.

    CBS ta ruwaito cewa Amurka da Isra'ila na duba yiwuwar kai hare-hare masu ƙarfi kan muhimman cibiyoyin makamashin Iran, yayin da Wall Street Journal ta ce Trump ya amince da wani sabon shiri domin ƙara matsin lamba ga Tehran.

    Fadar White House ba ta tabbatar da rahotannin kai hare-haren ba kai tsaye, amma kuma ba ta musanta su ba, tana mai jaddada cewa Amurka ba za ta bari Iran ta mallaki makamin nukiliya ba.

    Yayin da yaƙin Iran ya shiga wata na shida, har yanzu ɓangarorin biyu na ci gaba da tsayawa kan matsayinsu, inda Amurka ke neman Iran ta dakatar da shirinta na nukiliya, yayin da Tehran ta ƙi ja da baya.

  3. Farashin mai ya ƙaru saboda fargabar cikas ga jigilar mai ta Mashigar Hormuz

    Farashin ɗanyen mai ya tashi a kasuwannin duniya bayan fargabar cewa rikicin da ke yankin zai iya haddasa cikas ga jigilar mai ta Mashigar Hormuz, wata muhimmiyar hanyar da ake amfani da ita wajen safarar mai.

    Farashin ɗanyen mai na Brent ya ƙaru da kashi 1.2 cikin ɗari zuwa dala 90.12 kan ganga, yayin da ɗanyen man Amurka ya tashi da kashi 1.3 cikin ɗari zuwa dala 84.67.

    Hauhawar farashin ta biyo bayan rahotannin cewa an dakatar da wasu jiragen dakon mai ko kuma aka tilasta musu sauya hanya ta mashigar Hormuz.

    Yaƙin Iran ya rage yawan zirga-zirgar jiragen ruwa a mashigar, yayin da barazanar mayaƙan Houthi kan jiragen ruwa a Bab al-Mandab ke ƙara jefa sauran hanyoyin fitar da mai cikin haɗari.

  4. Iran ta ce za ta rufe mashigar Hormuz idan Amurka ta ci gaba da kai hare-hare

    Sakataren Majalisar Tsaron Ƙasa ta Iran, Ali Akbar Zolghadr, ya ce Iran za ta rufe mashigar ruwa ta Hormuz idan Amurka ta ci gaba da kai hare-hare ko takaita zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin.

    Ya gargaɗi cewa hakan zai iya yin mummunan tasiri ga tattalin arzikin duniya, kasuwar makamashi da kuma Amurka.

    A lokaci guda, kafofin yaɗa labarai na Iran sun ruwaito cewa Tehran ta shirya wani faɗaɗɗen shiri na mayar da martani idan Amurka ta kai hari.

    Wani babban jami'in tsaro da ba a bayyana sunansa ba ya ce rahotannin yiwuwar harin Amurka da Isra'ila kan Iran "rashin hankali ne", yana mai cewa martanin Iran zai haɗa da kai hari kan muhimman cibiyoyin Isra'ila da na makamashin Amurka a yankin.

  5. Trump ya musanta zargin Iran da kutse kan tsarin samar da ruwa a Minnesota

    Shugaban Amurka Donald Trump ya ce bai yarda cewa Iran ce ke da hannu a kuste ta intanet da aka yi kan tsarin samar da ruwa na jihar Minnesota ba, duk da cewa wasu rahotanni sun nuna cewa wasu jami'an Amurka na zargin Tehran da hannu a lamarin.

    Da yake magana a wani taron majalisar ministocinsa, kamar yadda kamfanin dillancin labaran Reuters ya ruwaito, Trump ya ce: "Mun ji an yi kutse ta intanet a Minnesota kuma ana ɗora laifin kan Iran. Ni ban yarda da hakan ba."

    Maimakon haka, Trump ya dora alhakin kan jami'an jihar da Gwamnan Minnesota mai jam'iyyar Democrat, Tim Walz, ba tare da gabatar da wata hujja da ke goyon bayan zarginsa ba.

    A nasa martanin, Gwamna Tim Walz ya ce Donald Trump ya san waɗanda ke da alhakin kutsen, yana mai ƙara da cewa irin an samu iran waɗannan kusten a wasu jihohin Amurka ma.

  6. Assalamu alaikum!

    Masu bibiyar shafin labaran kai tsaye na BBC Hausa,Barkanmu da Safiya

    Kamar kodayaushe, za mu kawo maku labarai game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida ce ke fatan kasancewa da ku a daidai wannan lokacin.

    Za ku iya leƙawa shafukanmu na sada zumunta na facebook da X da kuma whatsapp domin karanta wasu labaran da kallon bidiyo da ma tafka muhawara.

    Ku kasance tare da mu.