Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya, Talata - 04/03/2025

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Haruna Kakangi da Ahmad Bawage

  1. Ƙungiyar ƙasashen Sahel ta bikin ɗaga tutar AES

    Shugaban majalisar mulkin sojin Nijar da takwarorinsa na Burkina Faso da Mali sun jagoranci bikin ɗaga tutar ƙungiyar ƙasashen Sahel (AES) a hukumance a fadarsu.

    An ɗaga tutar ƙungiyar ƙawancen ƙasashen Sahel ɗin a hukumance a wannan Litinin, kwanaki kaɗan bayan amincewa da ita.

    Tutar na ƙunshe da ƙudurin baiɗaya na al'ummar ƙasashen uku wajen tabbatar da ƴancin kai da zaman lafiya da kuma ci gaban yankin.

    Ƙaddamar da wannan tuta alama ce mai kyau ga ƙasashen na AES, wanda ke nuna sabon zamani na haɗin gwiwa da juriya ga mutanen Sahel.

    Shuwagabannin ƙasashen na AES Abdourahamane Tchiani da Ibrahim Traoré da Assimi Goïta, sun yi na'am ga wannan sabuwar alamar da suka kira ta "haɗin-kai.

    An gudanar da bukukuwan lokaci guda a Bamako da Ouagadougou da kuma Yamai, lamarin da ke nuna wani muhimmin mataki na tabbatar da wani gagarumin aiki: na tabbatar da wata ƙungiyar da za ta iya tinkarar kalubalen tsaro, tattalin arziki da kuma zamantakewa a yankin.

    Shuwagabannin ƙasashen uku sun saka hannu kan kafa "Kungiyar Ƙasashen Sahel" a ranar 6 ga Yuli, 2024, a ƙarshen taron ƙoli na farko na ƙawancen ƙasashen yammacin Afirka (AES).

    Ƙasashen sun ɗauki wannan mataki ne bayan lalacewar dangantaka da ƙungiyar Ecowas, wadda ƙasashen uku suka fice daga cikinta a watan Janairun 2025, inda suka zargi Faransa - tsohuwar uwargijiyarsu da amfani da ƙungiyar.

  2. Kocin Super Eagles ya saka sunan Ahmed Musa cikin tawagarsa

    Kocin tawagar ƙwallon ƙafa ta Najeriya Super Eagles, Eric Chelle, ya saka Ahmed Musa cikin zubin farko na jerin 'yanwasan da ya gayyata buga wasan neman gurbi a gasar Kofin Duniya.

    A yau Talata ne Super Eagles ta sanar da jerin domin buga wasanninta da Rwanda da kuma Zimbabwe na neman shiga gasar ta 2026 da za a buga a Amurka, da Canada da Mexico.

    Kyaftin ɗin na Super Eagles bai sake samun gayyatar buga wa Najeriya wasa ba tun bayan kammala gasar Kofin Ƙasashen Afirka a watan Fabrairun 2024, inda bai buga wasa ko ɗaya ba.

    Sai dai tun bayan fara kakar wasa ta bana, Musa ya ci wa ƙungiyarsa ta Kano Pillars ƙwallaye shida a gasar Firimiyar Najeriya.

    Saka sunansa a yanzu ba shi nufin tabbas zai buga wasannin, ganin cewa akwai jerin sunayen na ƙarshe da kociyan zai sake fitarwa.

  3. Mun shirya aiwatar da zango na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza - Isra'ila

    Isra'ila ta ce a shirye take ta fara aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza idan har aka janye gaba ɗaya sojojin da ke yankin tare da sakin mutanen da ake garkuwa da su.

    Ministan harkokin wajen Isra'ila ya shaida wa ƴan jarida cewa ƙungiyar Hamas tana samun kuɗaɗe ne daga agajin da ake kai wa yankin, yana mai kare matakin ƙasarsa na dakatar da kai kayan jin ƙai cikin Gaza.

    Shugaban hukumar tallafa wa 'yan gudun hijirar Falasɗinu ta Majalisar Ɗinkin Duniya ya nanata cewa matakin Isra'ila na jefa rayukan Falasɗinawa cikin garari.

    A ƙarshen makon da ya gabata ne wa'adin matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza ya cika.

    Abin da har yanzu ba a fayyace ba shi ne me za a iya yi da zai sa Hamas ta ajiye makamanta.

  4. Ana neman masu son shiga tseren gudun fanfalaki a Koriya ta Arewa

    Wani kamfanin tsara tafiye-tafiye da ke China ya buƙaci masu sha'awar gudun fanfalaki daga ƙasashen duniya su yi rajista domin shiga tseren da za a yi a birnin Pyongyang.

    Baya ga ƴan ƙasar Rasha, wannan ne karon farko da za a bai wa mutane daga ƙasar waje damar ziyaratar Koriya ta Arewa, tun daga 2019.

    Kasancewar ba gasa ce da aka bari kowa ya shiga ba, waɗanda suka yi rajista ne kawai za a ba su damar shiga tseren na biornin Pyongyang.

    Za a kwashi waɗanda suka yi rajistar ne daga birnin Beijing na ƙasar China.

    Tafiyar za ta ƙunshi damar zuwa yawon buɗe ido da shiga kasuwanni a birnin na Pyongyang.

    Wannan na zuwa ne bayan damar da aka bai wa masu yawon buɗe ido daga ƙasashen yamma na shiga birnin Rason da ke arewa maso gabashin ƙasar a makon da ya gabata.

  5. Baƙuwar cuta ta kashe mutum 53 a Kongo

    An ruwaito mutuwar mutum 53 sakamakon wata baƙuwar cuta da ta ɓulla a arewa maso yammacin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo.

    Ba a dai san musabbabin cutar ba kawo yanzu.

    Hukumar Lafiya ta Duniya ta ce barazanar yaɗuwar cutar zuwa ƙasashe ba shi da yawa.

    Ana kyautata zaton cewa mace-macen sun afku ne a watan Fabrairu, a ƙauyen Basankusa a lardin Equateur.

    Gwajin da aka yi ya nuna cewa ba cutar Ebola ba ce ko kuma Marburg.

    Yawancin waɗanda aka yi wa gwaji ya nuna cewa cutar na kama da zazzaɓin malaria.

  6. Wasu da ake zargin ƴan Boko Haram sun sace malamin jami'a a Borno

    Wasu da ake zargin ƴan ƙungiyar Boko Haram sun yi awon gaba da wani Farfesa na jami’ar sojoji ta Najeriya da ke garin Biu tare da wasu fasinjoji.

    Ƴan bindigar sun kama mutanen ne kan hanyar Damaturu zuwa garin Biu kusa da garin Kamuya.

    Wannan lamari dai ya tayar da hankalin jama’a a cikin jami’ar da kuma garin na Biu.

    Sai dai duk ƙoƙarin da aka yi domin ji daga ɓangaren ƴansandan jihar ta Borno bai yi nasara ba.

    Ita dai wannan hanyar ta kasance ɗaya daga cikin waɗanda aka fi yin garkuwa da jama'a a yankin sakamakon rashin kyawunta, a cewar al’ummar yankin.

  7. Mutum biyu sun ƙone ƙurmus a gobarar tankar mai a Oyo

    Wasu mutum biyu sun mutu a wata gobarar tankar mai da ta afku a wani gidan mai a jihar Oyo.

    Hukumar kashe gobara ta jihar ta ce lamarin ya faru ne a karamar hukumar Oluyole na jihar.

    Sanarwar ta hukumar ta fitar yau Talata ta tabbatar da afkuwar lamarin, inda ta ce "direban tankar da kuma yaronsa ne suka rasa ransu".

    Shugaban hukumar Yemi Akinyinka ya ce bayan samun labarin abin da ya faru ne suka aika jami'ansu don su je su kashe wutar da safiyar yau, kamar yadda gidan talabijin na Channels ta ruwaito.

    "Abin takaici direban tankar da kuma yaronsa sun ƙone ƙurmus," in ji Akinyinka.

    Bincike da aka gudanar zuwa yanzu ya nuna cewa tankar ta kwace wa direban bayan da burkinsa ya kasa aiki, abin da ya janyo ta kama da wuta.

  8. Ƙawayen Ukraine sun yi tir da matakin Amurka na daina ba ta makamai

    Ukraine da ƙawayenta sun yi Alla-wadai da matakin da shugaban Amurka Donald Trump ya ɗauka na dakatar da agajin soji da take bai wa Ukraine - amma Rasha ta yi maraba da matakin.

    Firaiministan Ukraine Denys Shmyhal ya ce sojojin ƙasar suna da kayan yaƙi da za su iya kare kansu duk da dakatar da agajin Amurka, kuma suna son ci gaba da aiki da Wahington.

    Fadar Kremlin ta kwatanta matakin na Amurka a matsayin abu mai kyau da zai kawo zaman lafiya, kuma ta buƙaci Amurkar da ta ɗage takunkuman da ta saka wa Rasha.

    Amurkawa sun ce Ukraine ta shirya ba da wasu yankunanta, sai dai ba su buƙaci wani abu ba wurin Moscow.

    Amurka ta kasance ja-gaba wajen bai wa Ukraine agajin soji bayan da taki amincewa da mamayar Rasha.

  9. 'Za mu yi tattaki zuwa Kinshasa idan sojin gwamnati suka far mana'

    Jagoran ƴan tawayen da suka ƙwace yankuna a gabashin Jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kwango ya yi barazanar yin tattakin kilomita 1,500 zuwa babban birnin ƙasar Kinshasa, idan har sojojin gwamnati suka kai musu hari.

    Shugaban M23 Corneille Nangaa ya kuma musanta cewa Rwanda ce ke mara musu baya, duk da cewa kwararrun Majalisar Ɗinkin Duniya sun tabbatar da hakan.

    "Ni mutumin Kongo ne kuma na yi imanin cewa mu ne kaɗai za mu iya magance matsalolin mu, ba wasu daga wata ƙasa ta daban ba," in ji shi.

    Ya dai ki yin tsokaci kan zargin cin zarafin fararen hula da ake yi wa sojojinsa.

  10. Yadda za ku ci gajiyar falalar watan Ramadan

    Albarkacin watan Ramadana, Sheikh Aminu Daurawa ya faɗi falalar watan da kuma yadda masu azumi za su iya samun albarkar wannan watan ta hanyar aikata wasu ayyuka na alheri.

  11. Kotu a Kano ta ɗaure ƴan TikTok biyu kan wallafa bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa

    Wata kotun majistre da ke zama a anguwar Norman's land a karamar hukumar Fagge a jihar Kano, ta ɗaure wasu ƴan TikTok biyu a gidan yari, bayan samunsu da laifin amfani da bidiyo mai ɗauke da kalaman batsa.

    Hukumar tace fina-finai ta jihar ta kama mutanen ne Ahmad Isa da Maryam Musa mazauna anguwar Ladanai da ke Hotoro Quarters, inda daga bisani ta miƙa su ga kotun, kamar yadda Jaridar Daily Trust ta ruwaito.

    Lauyan gwamnatin jihar ta Kano, Barrister Garzali Maigari Bichi, ya same su da aikata laifi da ya kunshi haɗa baki don aikata laifi da kuma wallafa hotunan bidiyo masu ɗauke da kalaman batsa a shafukan sada zumunta.

    Kotun ta ce bidiyon na rashin ɗa'a ya ci karo da addini da kuma tarbiyya a jihar ta Kano.

    Mutanen biyu sun amsa aikata laifin.

    Alkaliyar kotun, mai shari'a Hadiza Muhammad Hassan ta yanke musu hukuncin zama gidan yari na shekara ɗaya ko kuma zaɓin biyan tarar naira 100,000 kowannensu - ta kuma hore su da su zama mutanen kirki.

  12. Kremlin ta ce dakatar da agajin soji ga Ukraine zai kawo zaman lafiya

    A taron manema labarai da fadar Kremlin ta saba yi kowace rana, BBC ta tambayi mai magana da yawun shugaba Putin martanin Rasha kan dakatar da bai wa Ukraine tallafin soji da Amurka ta yi.

    "Eh, ya kamata mu duba bayanai kan lamarin," in ji Dmitry Peskov. "Idan har da gaske ne, to wannan shi ne mataki da zai saka Kyiv ta nemi cimma yarjejeniyar zaman lafiya."

    Peskov ya ƙara da cewa Amurka ce sahun gaba wajen samar wa Ukraine da makamai.

    "Idan Amurka ta daina ko dakatar da bai wa Ukraine agajin soji, hakan shi ne abu mafi dacewa da kuma zai kawo zaman lafiya," a cewarsa.

  13. Ana shirin gurfanar da mutum 40 kan zargin barazana ga tsaron ƙasa a Tunisiya

    A yau ne za a gurfanar da ƴan adawar siyasa a Tunisia kimanin su 40 da ake tuhuma da laifukan barazana ga tsaron ƙasa, a wata shari'ar da ƙungiyoyin kare hakkin bil adama suka kira bita da kullin siyasa.

    Waɗanda ake tuhumar dai sun haɗa da jami'an diflomasiyya da ƴan siyasa da lauyoyi da kuma ƴan jarida masu sukar shugaba Kais Saied.

    Zargin yi wa tsaron ƙasa zagon kasa da kuma na shiga ƙungiyar ƴan ta'adda na ɗauke da hukunci mai tsanani, ciki har da hukuncin kisa.

    Ana tsare da wasu ne tun shekarar 2023, yayin da wasu kuma suka gudu zuwa kasashen waje.

    Masu fafutukar kare hakkin bil adama sun yi kira da a gudanar da zanga-zanga a birnin Tunis don nuna adawa da shari'ar.

  14. Shugaban mulkin sojin Gabon ya ayyana aniyar tsayawa takarar shugaban ƙasa

    Shugaban gwamnatin mulkin soji a Gabon Janar Brice Oligui Nguema ya sanar da aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban ƙasa a zaɓen da ke tafe watan gobe.

    Nguema ya ƙwace iko da mulki ne a wani juyin mulki a 2023 wnada ya kawo karshen jagorancin iyalan Bongo da suka shafe tsawon lokaci suna mulki.

    Tun wannan lokaci ne ƙasar ta amince da sabon kundin mulki da kuma garanbawul wa dokar zaɓe - wanda masu suka suka ce an yi ne domin taimakawa shugaban mulkin sojin ƙasar wajen tsayawa takarar shugaban ƙasa.

    Nguema ya faɗa wa al'ummar Gabon ranar Litinin cewa ya yanke shawarar yin takara a zaben ranar 12 ga watan Afrilu "bayan duba na tsanaki da kuma kiraye-kirayen da yawa daga cikin ku".

    Da yake yi wa dandazon magoya baya jawabi a Libreville, babban birnin ƙasar cikin mamakon ruwan sama, ya ce a shirye yake wajen kyautata makomar ƙasar mai arzikin mai.

    "Ni mai gina ƙasa ne, kuma ina son goyon bayanku da jajircewarku wajen gina wannan ƙasa," in ji shugaban mulkin sojin, wanda ya cika shekara 50 da haihuwa.

    Sanarwar ta biyo raɗe-raɗe na tsawon watanni kan aniyarsa ta son tsayawa takarar shugaban ƙasa.

  15. Ƴansanda sun kama wani matashi kan zargin kashe mahaifiyarsa a Bauchi

    Rundunar ƴansanda a jihar Bauchi ta ce ta kama wani matashi kan zargin kashe mahaifiyarsa.

    Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴansandan jihar, CSP Ahmed Wakili ya fitar, ya ce lamarin ya faru ne ranar 24 ga watan Fabrairu a wata unguwa mai suna Abujan Kwata.

    Ya ce ana zargin matashin mai suna Safiyanu Dalhatu ɗan shekara 20, da amfani da taɓarya wajen lakaɗawa mahaifiyarsa duka har ta kai ga mutuwarta.

    "Matashin ya yi wa mahaifiyar tasa mai suna Salama Abdullahi mai shekara 40 munanan raunuka a hannu kuma ya yi mata jina-jina abin da ya kai ga mutuwarta," in ji sanarwar ƴansandan.

    CSP Wakili ya ce bayan samun rahoton abin da faru ne suka aika tawagar jami'ansu zuwa anguwar, inda suka ɗauki mahaifiyar matashin zuwa asibitin koyarwa na Abubakar Tafawa Balewa - inda wani likita ya tabbatar da mutuwarta.

    Ya ƙara da cewa suna riƙe da matashin a halin yanzu da kuma taɓaryar da ya yi amfani da ita domin ci gaba da bincike.

    Ya ce bayan kammala bincike ne za su miƙa wanda ake zargin hannun kotu domin yanke masa hukunci.

  16. Unicef ya zargi wasu mayaƙa da yi wa ƙananan yara fyaɗe a Sudan

    Asusun kula da ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya ce mutane masu ɗauke da makamai suna yi wa yara ƙanana fyaɗe da kuma lalata da su a yaƙin basasar Sudan.

    Kashi biyu cikin uku na waɗanda lamarin ya shafa yara mata ne, sai kashi ɗaya bisa uku kuma suka kasance maza, abu mafi ɗaga hankali kuma shi ne guda 16 sun kasance yara ƴan kasa da shekaru biyar, ciki har da jarirai huɗu.

    Yayin da UNICEF ba ta zargi wani ɓangare da aikata laifin ba, wasu rahotanni na MDD sun fi nuna yatsa ne ga dakaraun ƙungiyar RSF da ake zargi da amfani da cin zarafin mata a matsayin makamin yaƙi.

  17. Shugabannin ƙasashen Larabawa za su yi taron gaggawa kan sake gina Gaza

    Shugabannin ƙasashen Larabawa za su gudanar da wani taron gaggawa a birnin Alkahira domin gabatar da shirinsu na sake gina Gaza.

    Suna dai fuskantar matsin lamba a kan su fito da wani tsarin da ya bambanta da shawarar da shugaba Trump ya bayar na karɓe yankin tare da sauyawa al'ummar Falasɗinawa matsuguni.

    Majiyoyin diflomasiyya da su ka ga kudurin da Masar za ta gabatar sun ce ya ba da shawarar kafa wani kwamitin wucin gadi da zai tafiyar da al'amuran Gaza da zarar an kawo karshen yaƙin Isra'ila da Hamas.

    Kudurin dai bai kunshi cikakkun bayanai kan batutuwa masu sarƙaƙiya ba da suka haɗa da wanda zai biya kuɗin sake gina yankin.

  18. Trump ya dakatar da agajin soji da Amurka ke bai wa Ukraine

    Jami'an gwamnatin Amurka sun ce shugaba Trump ya ba da umarnin dakatar da duk wani agajin soji da ake bai wa Ukraine.

    Matakin dai na zuwa ne kwanaki kaɗan bayan cacar bakin da Mista Trump ya yi da shugaba Zelensky a fadar White House.

    Ana tunanin umarnin - wanda zai fara aiki nan take - zai shafi makamai da alburusai na miliyoyin daloli da aka ware don kai wa Ukraine a cikin kwanakin karshe na gwamnatin Biden.

    Tun da farko a jiya Litinin Shugaba Trump ya caccaki Mista Zelensky a bainar jama'a - yana mai cewa ba zai daɗe a kan karagar mulki ba idan har bai goyi bayan yarjejeniyar zaman lafiya ba.

  19. Buɗewa

    Masu bibiyar mu barkan mu da safiyar Talata.

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa.

    Ku kasance da mu domin samun labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Ahmad Bawage ne zai jagoranci kawo muku labaran a wannan safiya bisa kulawar Haruna Kakangi.